Judith Uwizeye

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Judith Uwizeye
Minister in the Office of the President (en) Fassara

31 ga Augusta, 2017 -
Rayuwa
Haihuwa Ruwanda, 20 ga Augusta, 1979 (44 shekaru)
ƙasa Ruwanda
Mazauni Kigali
Karatu
Makaranta National University of Rwanda (en) Fassara
University of Groningen (en) Fassara
Sana'a
Sana'a Lauya, ɗan siyasa da Malami

Judith Uwizeye Lauya ce, Malama kuma 'yar siyasa a ƙasar Rwanda, wacce ta yi aiki a matsayin Minista a ofishin shugaban ƙasa, tun daga ranar 31 ga watan Agusta 2017.[1] Daga watan Yuli 2014 har zuwa Agusta 2017, ta yi aiki a matsayin ministar hidimar jama'a da aiki a majalisar ministocin Rwanda.[2][3]

Fage[gyara sashe | gyara masomin]

An haife ta a Ruwanda, a ranar 20 ga watan Agusta 1979.[2] Ta samu digirin digirgir a fannin shari'a a jami'ar ƙasar Rwanda a shekarar 2006. Daga nan ta wuce Jami'ar Groningen da ke ƙasar Netherlands inda ta kammala karatun digiri na biyu a fannin tattalin arziki da kasuwanci na ƙasa da ƙasa.[2][3]

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin shekara ta 2006, Uwizeye ta fara koyarwa a tsangayar shari'a a Jami'ar Ƙasa ta Ruwanda ta lokacin, a Huye.[2] Cibiyar ta haɗu da sauran manyan makarantun koyo don zama Jami'ar Ruwanda. A lokacin da aka naɗa ta minista a shekarar 2014, ta kai matsayin mataimakiyar laccara, a fannin tattalin arziki da kasuwanci na ƙasa da ƙasa.[2][3]

Na sirri[gyara sashe | gyara masomin]

Judith Uwizeye ta auri Manase Ntihinyurwa, jami'in kwastam na hukumar tara haraji ta Rwanda, kuma sun haifi yara guda biyu.

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

  • Majalisar Rwanda
  • Rosemary Mbabazi

Hanyoyin haɗi na waje[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Kimenyi, Felly (31 August 2017). "Rwanda gets new Cabinet, who is in?". New Times (Rwanda). Kigali. Retrieved 1 September 2017.
  2. 2.0 2.1 2.2 2.3 2.4 Umutesi, Doreen (31 July 2014). "Meet the new female faces in cabinet". New Times (Rwanda). Kigali. Retrieved 31 August 2017.
  3. 3.0 3.1 3.2 Jean Baptiste Micomyiza (24 July 2014). "CASS staff Member becomes Minister in the New Cabinet". Kigali: University of Rwanda, College of Arts and Social Sciences (CASS). Retrieved 31 August 2017.