Jump to content

Kala/Balge

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Kala/Balge

Wuri
Map
 12°18′N 14°30′E / 12.3°N 14.5°E / 12.3; 14.5
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
Jihohin NajeriyaJihar Borno
Yawan mutane
Faɗi 60,834 (2006)
• Yawan mutane 32.09 mazaunan/km²
Labarin ƙasa
Yawan fili 1,896 km²

Kala Balge Karamar hukuma ce dake a Jihar Borno Nijeriya.

Yawan Jama'a

[gyara sashe | gyara masomin]

A cewar ƙidayar shekarar 2006, Kala-Balge na da yawan jama'a 60,797. Kabilun da suka fi yawa a yankin sun haɗa da Kanuri, Shuwa Arab da wasu ƙananan kabilu. Addinin Musulunci shi ne mafi rinjaye, sai kuma wasu ’yan Kirista a ƙanƙance.

Tattalin Arziki

[gyara sashe | gyara masomin]

Mutanen Kala-Balge suna da sana'o’in noma, kiwo da kamun kifi. Ana noma gero, dawa, masara da wake a lokacin damina. Kogunan da ke kusa da yankin suna taimakawa sosai wajen kamun kifi.

Sakamakon kasancewar yankin a iyakar Najeriya da Kamaru, ana samun cinikayya da musayar kaya tsakanin kasashen, sai dai matsalolin tsaro sun kawo cikas ga harkokin kasuwanci.

Kalubale na Tsaro

[gyara sashe | gyara masomin]

Kala-Balge na daya daga cikin wuraren da suka fi shan wahala sakamakon tashe-tashen hankula da kungiyar Boko Haram. An samu hare-hare da dama a yankin, wanda ya tilasta dubban mutane tserewa zuwa sansanonin ’yan gudun hijira (IDP).

A shekarar 2017, wani mummunan lamari ya faru a Rann, inda jirgin sama na sojojin Najeriya ya kai harin bam da kuskure a sansanin ’yan gudun hijira, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar fiye da mutane 100 ciki har da ma’aikatan agaji. Wannan lamari ya ja hankalin duniya baki ɗaya.

Abubuwan More Rayuwa

[gyara sashe | gyara masomin]

Hanyoyin mota zuwa Kala-Balge ba su da kyau, musamman a lokacin damina, wanda ke haifar da ƙalubale ga kai agaji. Garin Rann na fama da ƙarancin asibitoci, makarantu da lantarki, kuma yana dogaro ne ga taimakon ƙungiyoyin agaji.

Wannan Muƙalar guntuwa ce: tana buƙatar a inganta ta, kuna iya gyara ta.