Kenneth Ogba

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Kenneth Ogba
Rayuwa
Mutuwa 27 ga Yuni, 2021
Sana'a

Kenneth Edafe Ogba (1966/1967 – 27 ga watan Yunin 2021) ɗan siyasar Najeriya ne kuma ɗan majalisar dokokin jihar Delta mai wakiltar mazaɓar Isoko ta kudu 1 a majalisar dokokin jihar Delta ta 7.

Sana'ar siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

A ranar 9 ga watan Maris ɗin 2019, Kenneth Edafe Ogba, mai wakiltar Peoples Democratic Party ya doke Okiemute Essien na jam'iyyar All Progressives Congress kuma ya lashe kujerar wakiltar mazaɓar Isoko ta kudu 1 a majalisar dokokin jihar Delta. Ya samu ƙuri'u 15,973, yayin da Essien ya samu ƙuri'u 7,323.[1][2][3]

A ranar 10 ga watan Yunin 2019, Ogba ya maye gurbin Orezi Esievo a majalisar dokokin jihar Delta.[4][5]

Rayuwa ta sirri[gyara sashe | gyara masomin]

Ogba daga Oleh, Isoko South, Jihar Delta, Nigeria. Mahaifinsa Lucky Ogba.[6]

Mutuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Ogba ya mutu a ranar 27 ga watan Yunin 2021 a Oleh, Isoko South, jihar Delta, Najeriya.[7]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]