Kisan gilla a Gamboru Ngala, 2014

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdevenimentKisan gilla a Gamboru Ngala, 2014
Map
 12°20′31″N 14°11′12″E / 12.3419°N 14.1867°E / 12.3419; 14.1867
Iri aukuwa
Kwanan watan 5 Mayu 2014
Wuri Gamboru

A daren ranar 5-6 ga watan Mayun 2014, mayaƙan Boko Haram sun kai hari a tagwayen garuruwan Gamboru da Ngala a jihar Borno, arewa maso gabashin Najeriya.[1] Kimanin mazauna garin 310 ne aka kashe a kisan a harin na tsawon sa’o’i 12, kuma an lalata garin sosai.[2][3][1]

A cikin wannan dare ne Boko Haram suka sace ƴan mata takwas masu shekaru tsakanin 12-15 daga arewa maso gabashin Najeriya,[4][5] daga baya adaɗin ya kai goma sha ɗaya.[6]

Bayan fage[gyara sashe | gyara masomin]

Akwai Gamboru jami’an tsaro a sansanin Ngala da suka bar garin kafin a kai harin domin bibiyar waɗanda suka yi garkuwa da ‘yan matan makarantar Chibok.[7]

Ana kallon jihar Borno a matsayin babbar cibiyar Boko Haram.[7] A cewar Sanatan Najeriya Ahmed Zanna da wasu mazauna garin, jami'an tsaron sun bar Gamboru Ngala ne bayan da mayakan Boko Haram suka yaɗa jita-jita cewa an ga ƴan matan makarantar da aka yi garkuwa da su.[8]

Kisa[gyara sashe | gyara masomin]

Ƴan ta’addar ɗauke da bindigogi kirar AK-47 da RPG, sun kai hari a garin kan wasu motoci sulke guda biyu da suka sace daga hannun sojojin Najeriya watanni da dama da suka gabata.[9] Ƴan ta’addan sun buɗe wuta kan mutanen a wata kasuwa mai cike da cunkoson jama’a da ake buɗewa da daddare lokacin da yanayin zafi ya kwanta.[10] Bayan ƙona gidaje, mayakan sun bindige mutanen da suka yi ƙoƙarin tserewa daga gobarar.[2]

An fara gano adadin waɗanda suka mutu a hukumance su 200 a ranar 7 ga watan Mayu. Zanna da Waziri Hassan wasu mazaunin yankin duk sun ba da rahoton mutuwar aƙalla mutane 336.[9]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 de Montclos, Marc-Antoine Pérouse (2017-05-08), "Boko Haram", Understanding Boko Haram, Routledge, pp. 19–40, doi:10.4324/9781315525051-2, ISBN 978-1-315-52505-1, retrieved 2020-05-16
  2. 2.0 2.1 "Boko Haram Attack Kills Hundreds In Border Town". The Huffington Post. Retrieved 7 May 2014.
  3. "Terrorism survivor in Cameroon takes road to recovery: UN News special report". UN News (in Turanci). 2019-08-19. Retrieved 2020-02-05.
  4. "Boko Haram kidnaps more girls in Nigeria", ABC, AU, 6 May 2014
  5. Suspected Boko Haram gunmen kidnap eight girls from village in Nigeria. Monica Mark, The Guardian website; Tuesday 6 May 2014 19.21 BST.
  6. Boko Haram kidnaps more children, kills villagers in Nigeria. Sabrina Ford, Laura Italiano and Post Wires; New York Post, May 11, 2014 | 1:35am.
  7. 7.0 7.1 Жертвами нападения "Боко Харам" на город в Нигерии стали 300 человек (in Russian). RIA Novosti. Retrieved 7 May 2014.CS1 maint: unrecognized language (link)
  8. "Nigeria confirms market massacre blamed on Boko Haram". BBC. Retrieved 10 May 2014.
  9. 9.0 9.1 Adam Nossiter. "Islamist Militants Kill Hundreds of Civilians in Northeastern Nigeria". The New York Times. Retrieved 10 May 2014.
  10. "Nigerian official: Hundreds killed in attack". The Washington Post. Archived from the original on 8 May 2014. Retrieved 7 May 2014.