Jump to content

Ministocin Muhammadu Buhari na farkon Mulki (2015)

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ministocin Muhammadu Buhari na farkon Mulki (2015)
Majalisun Najeriya
Bayanai
Farawa Satumba 2015
Applies to jurisdiction (en) Fassara Najeriya
Wanda ya biyo bayanshi Second Cabinet of President Muhammadu Buhari (en) Fassara
Wanda yake bi Second Cabinet of President Goodluck Jonathan (en) Fassara
Dissolved, abolished or demolished date (en) Fassara 28 Mayu 2019

Majalisar ministocin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta farko ta kunshi ministocin da aka nada a gwamnatin Buhari domin daukar nauyin kowace ma'aikatun gwamnatin Najeriya bayan zaben shekarar 2015. An rantsar da yawancin ministocin ne a ranar 11 ga watan Nuwamban shekarar 2015 sannan an rusa majalisar ministocin a ranar 28 ga watan Mayun shekarar 2019, kwana guda bayan rantsar da Buhari karo na biyu a matsayin shugaban kasa.[1][2][3][4]

A wata hira da jaridar Vanguard ta buga a ranar 19 ga Afrilu, 2015, Buhari, wanda gwamnatinsa za ta fara aiki a ranar 29 ga Mayu,shekara ta 2015, ya ce zai hada karamar majalisar ministocin da za ta yi aiki kafin bikin nadin sabbin ministocin a hukumance. A ranar 31 ga watan Mayun shekarar 2015 ne aka ruwaito Buhari ya ce zai karya al’adar jam’iyyar PDP inda gwamnoni ke nada ministoci. Zai nemo mutanen da suka cancanta, masu sadaukarwa da gogewa domin yin aiki tare dasu. [5] A ranar 1 ga watan Yuli, shekara ta 2015 mai magana da yawun shugaban ya ce Buhari zai jinkirta zaben majalisar ministoci har zuwa watan Satumba. Ya so ya kawar da cin hanci da rashawa kafin a nada sabbin ministoci. Wani mai magana da yawun Shugaban ya ce, jinkirin ba wani abu ba ne, idan aka kwatanta da kafa majalisar ministocin da aka yi a baya. Sai dai wani masanin tattalin arziki da ke Landan ya ce jinkirin ba zai samu karbuwa sosai daga masu zuba jari ba.[6]++ A daren ranar 30 ga watan Satumba ne jaridar TheCable ta yanar gizo a Najeriya ta ruwaito jerin sunayen mutane 21 da aka mikawa shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki domin tantancewa tare da tantance su. A ranar 11 ga watan Nuwamba, an rantsar da majalisar ministoci mai wakilai 36 daga kowace jiha daga cikin jihohi 36 na Najeriya.[7][8][9][10][11][12][13][14][15][16][17][18][19][20]









Mnistoci da Mukamansu

[gyara sashe | gyara masomin]

karin bayani

[gyara sashe | gyara masomin]
  1. https://www.bbc.com/hausa/news/2015/10/151006_nigeria_ministers_list
  2. Chris Kay (2015-07-01). "Buhari Delays Nigerian Cabinet Appointments to September". Bloomberg. Retrieved 2015-07-02.
  3. EXCLUSIVE: Fashola, Amaechi, Ngige, Onu, Lai, Kachikwu make Buhari's ministerial list - TheCable". TheCable. 2015-09-30. Retrieved 2018-04-26
  4. Omololu Ogunmade (2015-10-01). "Buhari's Team of Champions Unveiled". This Day. Abuja. Archived from the original (Web) on 2015-10-05. Retrieved 5 October 2015.
  5. Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named "AngelaDavis201505".
  6. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2022-10-17. Retrieved 2022-10-16.
  7. Nigeria's Buhari swears 36 ministers into cabinet after five-month wait". Reuters. 2015-11-11. Retrieved 2022-05-23.
  8. Inyang, Ifreke. "Buhari sacks Babachir Lawal as SGF, replaces him with Boss Mustapha". Daily Post. Lagos, Nigeria. Retrieved 30 January 2022.
  9. Tukur, Sani. "Buhari suspends SGF Babachir Lawal, DG NIA, Ayodele Oke". Premium Times. Retrieved 30 January 2022.
  10. Funkeye, Kelvin (20 September 2018). "Zainab Ahmed resigns from Budget Ministry, now Minister of Finance". TBC News. Retrieved 30 January 2022.
  11. Alade, Abiodun. "Ministers Who Resigned Under Buhari's Administration". Daily Trust. Retrieved 30 January 2022
  12. "Minister of environment resigns". TheCable. Retrieved 30 January 2022.
  13. PHOTO NEWS: Finance Minister Adeosun picks up APC membership card". Premium Times. Retrieved 30 January 2022.
  14. Kemi Adeosun: Nigeria minister resigns over forged certificate". BBC. Retrieved 30 January 2022.
  15. Minister of State for Foreign Affairs, Khadija Abba-Ibrahim, Resigns". This Day. Retrieved 30 January 2022
  16. George, Taiwo. "Labour minister Ocholi, wife, son die in road accident caused by burst tyres". TheCable. Retrieved 30 January 2022.
  17. Ogundipe, Samuel. "Ekiti 2018: Fayemi resigns as minister". Premium Times. Retrieved 30 January 2022.
  18. Nigerian president Muhammadu Buhari to become oil minister in own cabinet". The Guardian. Retrieved 30 January 2022.
  19. Ogundipe, Samuel. "'Mama Taraba' resigns as Buhari's women affairs minister". Premium Times. Retrieved 30 January 2022.
  20. About the Ministry". Ministry of Youth and Sports Development. Retrieved 30 January 2022.