Oluwole Oke

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Oluwole Oke
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

11 ga Yuni, 2019 -
District: Obokun/Oriade
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

Rayuwa
Haihuwa 28 ga Afirilu, 1967 (56 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta University of Abuja (en) Fassara
Jami'ar Obafemi Awolowo
University of London (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da ɗan kasuwa
Imani
Jam'iyar siyasa People's Democracy Party (en) Fassara

Oluwole Busayo Oke (an haife shi a 28 ga watan Afrilu 1967) ɗan kasuwan Najeriya ne, mai gudanarwa, masanin tattalin arziki kuma ɗan siyasa wanda ke aiki a Majalisar Wakilai ta 8 kuma ta yanzu.[1] Shi ne shugaban kwamitin asusun gwamnati a majalisar wakilan Najeriya mai wakiltar mazabar Obokun/Oriade na jihar Osun a karkashin jam'iyyar People's Democratic Party a Najeriya.[2][3]

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Oluwole Oke ya halarci kwalejin kimiyya da fasaha ta Ibadan, inda ya samu shaidar karatunsa na kasa a shekarar 1988 a fannin kasuwanci. Daga nan ya wuce Jami’ar Abuja inda ya sami digiri na farko a fannin tattalin arziki a shekarar 1999. Ya kuma yi karatun MBA daga fitaccen jami’ar Obafemi Awolowo University ile ife a shekarar 2004 A shekarar 2013, ya halarci Jami’ar Landan inda ya sami digiri na biyu.[4][5]

Aikin majalisa[gyara sashe | gyara masomin]

A shekarar 1999, an zabi Oke a majalisar wakilai ta Najeriya mai wakiltar mazabar Oriade / Obokun na jihar Osun. Oke ya yi aiki a matsayin memba kuma Shugaban Kwamitin Tsaro na Majalisar a tsakanin 2003 zuwa 2011. Ya yi rashin nasarar komawa kan kujerarsa a 2011, daga baya kuma ya sake tsayawa takara a 2015 kuma ya yi nasara. Bukatunsa na doka sun haɗa da ilimi, haraji, mai da iskar gas da sayayya.[6]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Assembly, Nigerian National. "National Assembly | Federal Republic of Nigeria". www.nass.gov.ng. Retrieved 19 March 2018.
  2. Nigeria Legislature 1861–2011: A Compendium of Members & Officials : a Special Publication in Commemoration of Nigeria at 50 (in Turanci). Department of Information and Publications, National Assembly. 1 January 2010. ISBN 9789789113262.
  3. "Reps give FMBN ex-boss 48 hours to render account". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2020-03-10. Retrieved 2022-02-21.
  4. Admin. "Hon Busayo Oluwole Oke". Osun govt. Archived from the original on 20 March 2018. Retrieved 19 March 2018.
  5. Admin. "Oluwole Oke". OluwoleOke. Archived from the original on 18 January 2018. Retrieved 19 March 2018.
  6. Admin. "Oke Busayo". Blerf. Retrieved 19 March 2018.