Rizky Ahmad Sanjaya Pellu (an haife shi a ranar 26 ga watan Yuni shekarar 1992) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne ɗan ƙasar Indonesiya wanda ke taka leda a matsayin ɗan wasan tsakiya a ƙungiyar RANS Nusantara ta La Liga 1, a kan aro daga PSM Makassar .
A cikin watan 2008, Rizky ya wakilci Indonesia U-16, a cikin watan 2008 AFC U-16 Championship . Rizky ya lashe wasansa na farko a Indonesia a wasan sada zumunci da Andorra a ranar 26 ga watan Maris, shekarar 2014.