Teemah Yola
Fatima Isa Muhammad wacce aka fi sani da Teemah Yola Jaruma ce a masana'antar shirya fina-finai na Hausa wato Kannywood da ke arewacin Najeriya.[1] jarumar ta yi suna sanadiyyar wani fim mai dogon zango, mai suna labarina.
Farkon rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]
An haifi Fatima a watan mayu 11 ga watan a shekarar 1993 a cikin garin Yola jihar Adamawa Nijeriya. Mahaifin ta shi yasata a makarantar firamare, bayan ta gama sakandiri ta sami shiga Jami'ar Maiduguri inda ta karanci harshen larabci.[2]
Sana'ar fim[gyara sashe | gyara masomin]
Ta fara fitowa a wasan kwaikwayo tun a shekarar 2015 wanda yafi fito da ita shine fim din labarina Mai dogon zango
Fina-finai[gyara sashe | gyara masomin]
Ta yi fina finai da dama, amman an santa a fim wanda fim din 'labarina', wani fim da Aminu Saira ke bayar da Umarni.[3]
Ga wasu fina-finai;[4]
- Labarina
- Ukku sau ukku
- Dakin Amarya
- Ragon Azanci
- Gida ukku
- Tozarci. da sauransu
Rayuwar sirri[gyara sashe | gyara masomin]
Fatima tayi aure inda ta haifi yara guda biyu, [ana buƙatar hujja] daga Nan ta rabu da mijinta ta shiga harkar fim gadan-gadan.
Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]
- ↑ https://www.bbc.com/hausa/media-57919897
- ↑ https://www.thefamousnaija.com/2020/09/fatima-teema-yola-biography-age-husband_4.html
- ↑ https://labarai.com.ng/gwanin-shaawa-a-karon-farko-teemah-yola-ta-bayyana-iyayenta-na-jini-da-yan-uwanta/
- ↑ https://www.northernwiki.com.ng/cikkakken-tarihin-teema-yola/