Víctor Guambe (an haife shi a ranar 8 ga watan Oktoban 1998) ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne ɗan ƙasar Mozambique wanda ke taka leda a matsayin mai tsaron gida ga Costa do Sol da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Mozambique.[1]
Guambe ya fara wasansa na farko a duniya a ranar 28 ga watan Yuni shekara ta 2017 a cikin nasara da ci 2–1 a kan Seychelles a gasar cin kofin COSAFA na shekarar 2017.[2]