Jump to content

Yan Brazil ƴan asalin Najeriya

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.

Dan Najeriya dan Brazil (Portuguese) ɗan ƙasar Brazil ne mai cikakken, ko galibin zuriyar Najeriya, ko kuma haifaffen Najeriya da ke zaune a Brazil.

Sama da ƴan Najeriya 90,000 da ke zaune ba bisa ka’ida ba a Brazil ba tare da cikakkun takardu ba kafin 1 ga watan Fabrairu, shekara ta 2019 za su amfana daga tayin afuwan da gwamnatin Brazil ta yi. Jakadan Najeriya a Brazil, Kayode Garrick ne ya bayyana haka ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a Brazil. Garrick, ya ce sama da ƴan Najeriya 2,000 da za su ci gajiyar sanarwar afuwa ta Brazil na daga cikin ƴan Najeriya 5,000 da ke zaune a ƙasar a halin yanzu. A watan Satumba na shekarar 2008, gwamnatin Najeriya ta buɗe gidan Casa da Nigeria ko "Gidan Al'adun Najeriya" a unguwar tarihi mai suna Pelourinho na Salvador, Bahia, tare da goyon bayan gwamnatocin Bahia da Brazil.

Matsalar wariyar launin fata, 2011

[gyara sashe | gyara masomin]

Wani batu na kyamar baki / wariyar launin fata da wani malamin jami'a ya yi wa wani ɗalibi ɗan Najeriya a Jami'ar Tarayya ta Maranhão ya girgiza ƙasar a tsakiyar Shekara ta 2011.[1] Daga baya dubban dalibai ne suka sanya hannu kan takardar korar Farfesan.[2]

  1. "Nigerian student says he will not go back to Africa, after polemics about racism" (in Harshen Potugis). São Paulo: G1. Retrieved 23 March 2012.
  2. "Students ask for dismissal of a teacher suspected of racism in Maranhão" (in Harshen Potugis). G1. Retrieved 23 March 2012.