Abdur Rahim (malamai)

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abdur Rahim (malamai)
Rayuwa
Haihuwa Pirojpur District (en) Fassara, 2 ga Maris, 1918
ƙasa Bangladash
British Raj (en) Fassara
Pakistan
Harshen uwa Bangla (en) Fassara
Mutuwa Dhaka, 1 Oktoba 1987
Karatu
Harsuna Bangla (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Addini Mabiya Sunnah
Jam'iyar siyasa Bangladesh Jamaat-e-Islami (en) Fassara

 

Mawlana Abdur Rahim (Bengali </link>;2 Maris 1918 -1 Oktoba 1987) malamin Islama ɗan ƙasar Bangladesh ne kuma sanannen ɗan siyasa a Kudancin Asiya, kuma ya fara tallata Jamaat-e-Islami Bangladesh.

Ya fassara litattafai da dama da fitattun malaman addinin musulunci kamar su Abul A'la Maududi da Yusuf al-Qaradawi suka rubuta zuwa harshen Bengali kuma da kansa yayi rubuce-rubuce da yawa kan tushen Musulunci cikin harshen Urdu da Bengali.

Rayuwar farko[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Mohammad Abdur Rahim a ƙauyen Shialkathi acikin wani fitaccen dangin Sheikhs, gundumar Pirojpur a Bangladesh, danginsa sun fito ne daga zuriyar Sheikh Baijeed, ɗan Darwish na Farisa. Mahaifinsa shine Haji Khabiruddin da mahaifiyarsa Aklimunness. Shine na hudu acikin yara goma sha biyu a gidan. Fitaccen dan uwansa shine babban yayansa ATM Abdul Wahid, wanda ya kammala karatu a makarantar Alia Madrasa ta Calcutta kuma fitaccen marubucin adabi. Biyu daga cikin ’yan uwansa, M.A Karim da M.A Sattar, su ma sanannun marubuta ne.[1]

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan ya kammala karatun shekaru hudu na farko a masallacin kauyen da ke kusa da gidansa, ya samu shigarsa a Madrasa Sharshina Aliya a 1934. A nan yayi karatu kusan shekara biyar. A shekara ta 1938 Abdur Rahim ya kammala karatunsa na kwarai daga Sharsina aliya Madrassah, sannan ya samu gurbin shiga Madrasa Aliya ta Calcutta (Jami'ar Aliah a halin yanzu) inda yaci jarrabawar Fazil da Kamil a 1940 da 1942, bi da bi.

Rawar a Jama'atu-e-Islami[gyara sashe | gyara masomin]

Abdur Rahim ya kasance yana karbar Mujallar Tarjamanul Qur'an wanda Abul A'la Maududi ya shirya a lokacin yana ɗalibi a Madrasa Aliya. Kasancewar wannan mujalla da sauran rubuce-rubucen Syed Abul A'la Maududi yayi tasiri matuka, Abdur Rahim ya halarci taron Jama'atu Islamiyya na Indiyawan da aka gudanar a garin Allahabad a shekara ta 1946, inda daga nan ne ya saba da jagororin Jama'a da dama. Daga baya ya shiga ƙungiyar a zaman 1946-47.

Abdur Rahim na daga cikin mutane hudu da suka fara aiki a Dhaka domin kafa tushen Jamaat-e-Islami a Bangladesh. Sauran sune Rafi Ahmed Indori, Khurshid Ahmed Bhat da Qari Jalil Ashrafi Nadwi. A cikin 1955, an zabi Abdur Rahim Ameer na Jamaat-e-Islami na Gabashin Pakistan. A cikin 1970, ya zama Nayeb-e-Ameer (mataimaki ko mataimakin shugaban kasa) na Jamaat-e-Islami Pakistan, yayin da Golam Azam aka zabi sabon Ameer na Jamaat-e-Islami Gabashin Pakistan. Shi ne shugaban Jamaat-e-Islami na Bangladesh na farko da aka zaɓa. A lokacin Yaƙin 'Yanci na 1971, ya kasance a makale a Pakistan bayan barkewar yaƙi kuma kawai ya sami damar komawa ƙasar acikin 1974. A tsakanin shekarun 1971-1978, an hana Jamaat shiga harkokin siyasa a Bangladesh.[2]

Ya taka rawa wajen kawo jam'iyyun siyasa daban-daban na Musulunci karkashin tutar jam'iyyar Islamic Democratic League (IDL), wacce ta lashe kujeru 20 a zaben 'yan majalisar dokokin da aka gudanar a ranar 18 ga Fabrairun 1979.

Littattafai[gyara sashe | gyara masomin]

Abdur Rahim ya rubuta littafai da dama a rayuwarsa. Wasu daga cikin littafansa sun haɗa da:

  1. Al-Qurane'r Aloke Unnoto Jiboner Adorsho [Ma'anar Ingantacciyar Hanyar Rayuwa a Hasken Al-Qur'ani, 1980].
  2. Ajker Chintadhara (Tsarin Tunanin Yau, 1980)
  3. Hadith Sharif (mujalladi 3)
  4. Hadisi Shongkoloner Itihash
  5. Pashchatto Shobbhotar Darshonik Bhitti (Tsarin Falsafa na wayewar Yamma, 1984)
  6. Al-Quran Nobuuet O Risalat [1984]
  7. Al-Quran Aloke Shirk O Towheed [1983]
  8. Al-Quran Rashtro O Shorkar [1988]
  9. Islamer Zakat Bidhan (1982-86)- fassarar littafin Yusuf Al Qaradawi
  10. Bingsho Shotabdir Jahliyat (1982-1986) - fassarar littafin Sayyid Qutb
  11. Tafheemul Quran, juzu'i 19- fassarar littafin Maududi
  12. Sunnatu Ya Bida'atu

Mutuwa[gyara sashe | gyara masomin]

A ranar 29 ga Satumba 1987, yayi rashin lafiya. An shigar da shi asibiti a ranar 30 ga Satumba, ya mutu a ranar 1 ga Oktoba 1987 a Dhaka.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named rahim
  2. Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named commonwealth