Aminata Boureima Takoubakoyé

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Aminata Boureima Takoubakoyé
Rayuwa
Haihuwa Niamey, 23 Satumba 1979 (44 shekaru)
ƙasa Nijar
Karatu
Harsuna Faransanci
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da Mai tattala arziki

Aminata Takoubakoyé Takoubakoyé (an haifeta a ranar 23 ga Satumban shekarar 1979, a Niamey, Niger ) ƴar Nijar ce kuma ƴar siyasa. Tsakanin Fabrairun shekarar 2010 zuwa Afrilu 2011, Takoubakoyé ta jagoranci Ma'aikatar Sadarwa da Fasahar Sadarwa da Al'adu a cikin Gwamnatin Riƙon ƙwarya ta Rundunar Soja ta Majalisar Ƙoli don Maido da Dimokuraɗiyya.[1][2]

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan dawowarta Nijar bayan ta yi karatu a Rabat, a Morocco, Aminata Takoubakoyé ta karɓi muƙamin ƙwararre a hukumar tattara kuɗaɗen shiga ta ƙasa a cibiyar ƙididdiga ta Nijar. Daga Afrilun Shekarar 2004 zuwa Satumba 2009, ta kasance Jami'ar Watsa Labarai da Taimako a Sakatariyar Dindindin na Tsarin Dabarun Rage Talauci (Secrétariat Permanent de la Stratégie de Réduction de la Pauvreté). Daga bisani, daga Satumba 2009 zuwa Maris 2010, Takoubakoyé ta kasance mai gudanarwa a National Observatory for Poverty (Observatoire National de la Pauvreté). A watan Maris na 2010, Janar Salou Djibo, babban kwamandan sojojin Nijar, ya naɗa ta a gwamnatin riƙon ƙwarya kuma ya ba ta amanar sashen sadarwa, sabbin fasahohin yaɗa labarai da al'adu. Ta riƙe ofishin har zuwa Afrilu 2011.[3]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]