Annouscka Brummelda Kordom (an haife ta a ranar 12 ga watan Agusta 1997)[1] 'yar wasan ƙwallon ƙafa ce ta Namibia wacce ke taka leda a matsayin 'yar wasan gaba ga ƙungiyar mata ta ƙasar Namibia.[2] Ta kasance cikin tawagar a gasar cin kofin matan Afirka ta shekarar 2014.[3] A matakin kulob ta buga wasa a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta JS Academy a Namibia.[4] Ta yi wasan ƙwallon ƙafa na kwaleji a Jami'ar Corban da ke Amurka.[5][6]