Azubuike Okechukwu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Azubuike Okechukwu
Rayuwa
Haihuwa Katsina, 19 ga Afirilu, 1997 (26 shekaru)
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
Yeni Malatyaspor (en) Fassara-
Bayelsa United F.C.2012-2015
Yeni Malatyaspor (en) Fassara2015-
 
Muƙami ko ƙwarewa Mai buga tsakiya
Lamban wasa 14
Nauyi 68 kg
Tsayi 170 cm
Azubuike Godson Okechukwu a yayin fafatawa

Azubuike Godson Okechukwu (An haife shi ranar 19 ga watan Afrilu, 1997). ɗan wasan ƙwallon ƙafa ta ƙasar Najeriya da ke buga ƙwallo a ƙungiyar clubstanbul Başakşehir ta kasar Turkiyya a matsayin ɗan wasan tsakiya.

Tashe[gyara sashe | gyara masomin]

An haifeshi a Katsina, Okechukwu ya bugawa ƙungiyoyin Bayelsa United da Yeni Malatyaspor ƙwallon ƙafa.

A ranar 19 ga watan Agusta 2018, Okechukwu ya koma ƙungiyar Pyramids FC ta Premier ta Masar.[1][2]

A watan Janairun 2019, ya koma Çaykur Rizespor a matsayin aro har zuwa karshen kakar wasa ta bana. A ranar 10 ga Yulin 2019, İstanbul Başakşehir ya tabbatar, cewa sun sanya hannu kan Okechukwu kan yarjejeniyar aro na tsawon lokaci. [3] Ya lashe gasar ta Turkiyya tare da kulab din.

A watan Agusta na 2020, Okechukwu ya sanya hannu kan kwangilar dindindin tare da İstanbul Başakşehir.

Ƙungiyoyin Duniya[gyara sashe | gyara masomin]

Okechukwu ya fara buga wa ƙasar wasa ne a ƙungiyar kwallon kafa ta kasa a shekarar 2016, kuma Najeriya ce ta zabe shi a cikin jerin 'yan wasa 35 na wucin gadi da za su buga gasar Olympics ta bazara ta 2016.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]