Bouli Ali Diallo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Bouli Ali Diallo
Rayuwa
Haihuwa Nijar, 1948 (75/76 shekaru)
ƙasa Nijar
Karatu
Makaranta Université Cheikh Anta Diop (en) Fassara
Montpellier 2 University (en) Fassara
Harsuna Faransanci
Sana'a
Sana'a Malami, gwagwarmaya da ɗan siyasa

Bouli Ali Diallo (an haifeta a shekarar 1948) malamar jami'a ce kuma yar gwagwarmaya yaryar jamhuriyar Nijar.

Rayuwa da tashe[gyara sashe | gyara masomin]

Ali Diallo ta halarci makarantun horo kan koyarwa da dama ciki harda makarantar horar da malamai ta Tillabéri, wadda a lokacin itace kadai mace daliba a makarantar. Daganan tawuce jami'ar Dhakar inda ta karanta Kimiyya kuma har ta samu digiri a shekarar 1978, da kuma Jami'ar kimiyya da fasaha ta Languedoc a garin Montpellier, inda ta kammala digirin digirgir a shekarar 1991.[1]

Ta dawo Nijar domin ta koyar da ilimin kimiyyar halitta a Jami'ar Abdou Moumouni University, [2] aikin da tafara tun daga shekarar 1978. Tayi aiyuka da dama, daga ciki akwai; daga shekarar 1987 zuwa shekarar 1993 tarike matsayin darakta a ma'aikatar harkokin waje, ta rike mukamin ministar ilimi ta kasa a shekarar 1995 zuwa shekarar 1996.

Ta zama mamba a hukumomin Institut de recherche pour le développement da Aide et Action sannan daga shekarar 1999 zuwa shekarar 2004 ta shugabanci kungiyoyin dake fafutikar ganin an ilimantar da mata a Afrika. Tasha karbar lambobin yabo daga kasar Faransa ciki harda ta Ordre des Palmes Académiques.[1] She has remained an activist in Niger, speaking on the need to develop educational opportunities for women.[2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 Abdourahmane Idrissa; Samuel Decalo (1 June 2012). Historical Dictionary of Niger. Scarecrow Press. ISBN 978-0-8108-7090-1.
  2. 2.0 2.1 Alison Behnke (15 December 2007). Niger in Pictures. Twenty-First Century Books. pp. 70–. ISBN 978-0-8225-7147-6.