Nijar (ƙasa)
|
|||||
|
| |||||
|
| |||||
| Take |
L'Honneur de la Patrie (mul) | ||||
|
| |||||
| Kirari |
«Fraternité, Travail, Progrès» «Fraternity, Work, Progress» «Братство, труд, прогрес» «Brawdoliaeth, Gwaith, Datblygiad» | ||||
| Suna saboda | Nijar | ||||
| Wuri | |||||
| |||||
| Babban birni | Niamey | ||||
| Yawan mutane | |||||
| Faɗi | 21,477,348 (2017) | ||||
| • Yawan mutane | 16.95 mazaunan/km² | ||||
| Harshen gwamnati | Hausa | ||||
| Labarin ƙasa | |||||
| Bangare na | Afirka ta Yamma | ||||
| Yawan fili | 1,267,000 km² | ||||
| Wuri mafi tsayi | Mont Idoukal-n-Taghès (2,022 m) | ||||
| Wuri mafi ƙasa | Nijar (200 m) | ||||
| Sun raba iyaka da | |||||
| Bayanan tarihi | |||||
| Mabiyi | Faransanci Yammacin Afirka | ||||
| Ƙirƙira | 1960 | ||||
| Ranakun huta | |||||
| Tsarin Siyasa | |||||
| Majalisar zartarwa |
Cabinet of Niger (en) | ||||
| Gangar majalisa |
National Assembly (en) | ||||
| • shugaban Jamhuriyar Nijar | Abdourahamane Tchiani (28 ga Yuli, 2023) | ||||
| • Firaministan Jamhuriyar Nijar | Ali Lamine Zeine (8 ga Augusta, 2023) | ||||
| Ikonomi | |||||
| Nominal GDP (en) | 14,915,002,098 $ (2021) | ||||
| Kuɗi | CFA franc Yammacin Afirka | ||||
| Bayanan Tuntuɓa | |||||
| Kasancewa a yanki na lokaci | |||||
| Suna ta yanar gizo |
.ne (mul) | ||||
| Tsarin lamba ta kiran tarho | +227 | ||||
| Lambar taimakon gaggawa |
17 (mul) | ||||
| Lambar ƙasa | NE | ||||



Nijar ko Nijer[1][2] ƙasa ce da ke yankin Afrika ta Yamma. Tana maƙwabtaka da ƙasashe bakwai (Najeriya daga kudu, Libya daga arewa maso gabas, Aljeriya daga arewa maso yamma, Mali daga yamma, Burkina faso da Benin daga kudu maso yamma, Chadi daga gabas). Tana da al'umma da ta kai fiye da mutum miliyan sha bakwai (17) Kuma tana da ƙabilu daban-daban, kamar su: Hausawa, Zabarmawa, Abzinawa, Fulani, Kanuri, Bugaje, Barebari, Larabawa, Tubawa, da Gurmawa. Nijar ta na ɗaya daga cikin ƙasashen ƙungiyar tattalin arziƙin ƙasashen yammacin Africa. (CEDEAO). Nijar tana da faɗin ƙasa kimanin 1,270,000Km (490,000sq mi) ta biyu 2 a fadin ƙasa, a ƙasashen Afirka ta yamma. Wajan 80% na ƙasar saharah ne, wajan 22 million mutanan ƙasar Nijar musulmai ne

Nijar ta samu 'yancin kanta a shekara ta 1960 daga Turawan mulkin mallaka na kasar Faransa. Tana da arziƙin ma'adanai na cikin ƙasa kamar zinariya, da ƙarfe, da gawayi, da uranium, da kuma fetur.
Al'umman Nijar 2013
[gyara sashe | gyara masomin]A lissafin kasafin ƙasa da INS ta fitar [3], a shekara ta 2013, ƙasar Nijar tana da al'umma milyan sha bakwai da dubu ɗari da ashirin da tara da saba'in da shida (17,129,076).
Manyan Birane
[gyara sashe | gyara masomin]


Yankunan Gwamnatin kasar Sune kamar haka:
- Yankin Agadez
- Yankin Diffa
- Yankin Dosso
- Yankin Maradi
- Yankin Tahoua
- Yankin Tillabéri
- Yankin Zinder
- Niamey (Babban birni)
Birane da ke da adadin al'umma samada dubu goma (10,000) akan kidayar shekara ta 2012.
Masana da masu ruwa a tsaki da gwamnatin mulkin soji ta Jamhuriyar Nijar ta tara domin tsara makomar ƙasar sun kammala taron ƙasa da suka kwashe kwana biyar suna gudanarwa.[6]
Taron ya fara ne daga ranar Asabar 15 ga watan Fabarairu, zuwa Alhamis 20 ga watan na Fabarairu.[7]
Shugaban mulkin soji na ƙasar Abdourahamane Tchiani ne ya kira taron domin seta hanyar da ƙasar za ta bi a shekaru masu zuwa.[8]
Tun farko, bayan juyin mulkin da sojojin suka yi wa Mohammed Bazoum, gwamnatin sojin ta Nijar ta nuna alamun cewa za ta iya mayar da mulki ga farar hula cikin shekara uku, sai dai sakamakon taron ƙasar ya nuna akasin haka.[9]
Ga wasu daga cikin abubuwan da taron ya cimma:
Tabbatar da Tchina a matsayin shugaban ƙasa
[gyara sashe | gyara masomin]Taron haɗin kan ƙasar na Jamhuriyar Nijar ya amince da sauya yadda ake kiran jagoran juyin mulkin ƙasar zuwa 'shugaban ƙasa'.[10]
Taron ya ce ya cimma matsayar ne bayan la'akari da "jagorancin" da Tchiani ya nuna wajen sake ƙwato wa Nijar "ƴancinta".[11]
Gwamnatin riƙon ƙwarya ta shekara biyar
[gyara sashe | gyara masomin]Taron ƙasar ta Jamhuriyar Nijar ya amince da samar da gwamnatin riƙon ƙwarya ta tsawon shekara biyar, wadda ita ce za ta tsara yadda za a mayar da ƙasar kan tafarkin dimokuraɗiyya[12]
A lokacin gabatar da jawabi kan matsayar da taron ya cimma, ɗaya daga cikin jagororin taron, Bibata Niandou ta ce: "Miƙa mulki zai kasance a cikin wata 60, wato shekara biyar, daga ranar da aka amince da wannan tsari."[13]
Sai dai ta ƙara da bayanin cewa wa'adin da aka ɗiba na mayar da mulkin ga farar hula zai iya "sauyawa" bisa la'akari da "yanayin tsaro" a ƙasar.[14]
Takara
[gyara sashe | gyara masomin]Taron ya yarda cewa jagororin mulkin sojin ƙasar za su iya tsayawa takara a zaɓen da za a gudanar bayan shekara biyar na riƙon ƙwarya.[15]
Dama wannan na daga cikin manyan abubuwan da aka shirya samun matsaya a kan shi.[16]
Hakan na nufin shugaban mulkin soji na ƙasar a yanzu na da damar tsayawa takara.[17]
Wannan na daga cikin ɗabi'un shugabannin mulkin soji a nahiyar Afirka, inda sojojin da suka yi juyin mulki kan rikiɗe zuwa shugabannin farar hula ta hanyar zaɓe.[18]
Na baya-bayan nan shi ne zaɓen da aka yi wa Mahamat Idris Deby a matsayin shugaban ƙasa bayan kasancewarsa shugaban ƙasar soji sanadiyyar mutuwar mahaifinsa.[19]
Ƙara wa Tchiani muƙami
[gyara sashe | gyara masomin]Ɗaya daga cikin mataimakan shugaban taron, Abdoulaye Seydou ya kuma bayyana cewa taron ya amince da ƙara wa shugaban mulkin soji na ƙasar Abdourahamane Tchiani daga Birgediya-Janar zuwa Janar na soja.[20]
- Me ake tsammani daga babban taron ƙasa na Jamhuriyar Nijar?
- Ƙasashen da cin hanci da rashawa suka yi wa katutu a 2024 - Rahoto
- Me zai faru bayan ficewar ƙasashen Nijar da Mali da Burkina Faso daga Ecowas?
A yanzu dai za a gabatar wa majalisar mulkin sojin Jamhuriyar Nijar matsayra da taron ya cimma domin amincewa tare da ɗaukar matsaya ta ƙarshe.[21]
Taron ya ƙunshi mutane kimanin 700, waɗanda suka fito daga ɓangarori da dama na ƙasar, da suka haɗa da tsofaffin ministoci da masana da lauyoyi da sojoji da malamai da kuma ƴan ƙungiyoyi masu zaman kansu.[22]
Jamhuriyar Nijar na daga cikin ƙasashe uku - Burkina Faso, Mali da Nijar - waɗanda suka tsame kansu daga ƙungiyar ƙasashen yammacin Afirka, tun bayan juyin mulkin soji da suka faru a ƙasashen.[23]
Haka nan sun raba-gari da ƙasashen yammacin duniya, ciki har da uwar-gijiyarsu, Faransa, sannan suka karkata alaƙarsu zuwa Rasha.[24]
Hotuna
[gyara sashe | gyara masomin]-
Tutar kasar
-
Matasa yan ƙabilar Wodaabe a kasar
-
Akwai Sahara a kasar sosai
-
Coat of Arms
-
Nijar
-
Taswirar kasar
-
Kogin bank, Nijar
| Ƙasashen Afirka |
| Afirka ta Tsakiya | Aljeriya | Angola | Benin | Botswana | Burkina Faso | Burundi | Cabo Verde | Cadi | Côte d'Ivoire | Eritrea | eSwatini | Ethiopia | Gabon | Gambiya | Ghana | Gine | Gine Bisau | Ginen Ekweita | Jibuti | Kameru | Kenya | Komoros | Kwango (JK) | Kwango (JDK) | Laberiya | Lesotho | Libya | Madagaskar | Mali | Moris | Muritaniya | Misra | Morocco | Mozambik | Namibiya | Nijar | Nijeriya | Ruwanda | Saliyo | Sao Tome da Prinsipe | Senegal | Seychelles | Somaliya | Sudan | Sudan ta Kudu | Tanzaniya | Togo | Tunisiya | Uganda | Zambiya | Zimbabwe |
MAnazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "ISO 3166". ISO Online Browsing Platform. Archived from the original on 17 June 2016. Retrieved 12 May 2017.
- ↑ "UNGEGN World Geographical Names". United Nations Statisticsc Division. 1 March 2017. Archived from the original on 28 July 2011. Retrieved 12 May 2017.
- ↑ (http://www.stat-niger.org/statistique/)
- ↑ Population figures from citypopulation.de, citing (2001) Institut National de la Statistique du Niger.
- ↑ fallingrain.com.
- ↑ Bbc
- ↑ Bbc
- ↑ Bbc
- ↑ bbc
- ↑ Bbc
- ↑ Bbc
- ↑ bbc
- ↑ Bbc
- ↑ Bbc
- ↑ Bbc
- ↑ bbc
- ↑ bbc
- ↑ bbc
- ↑ bbc
- ↑ bbc
- ↑ Bbc
- ↑ Bbc
- ↑ bbc
- ↑ Bbc
