Clara Bata Ogunbiyi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Clara Bata Ogunbiyi
Rayuwa
Haihuwa Jihar Borno, 27 ga Faburairu, 1948 (76 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta University of Hull (en) Fassara
Jami'ar Ahmadu Bello
Jami'ar Maiduguri
Sana'a
Sana'a masana

Clara Bata Ogunbiyi (An haife ta ranar 27th, Fabrairu 1948), a Lassa, jihar Borno. Ta halarci makarantar firamare ta Lassa tsakanin 1955 da 1958 daga nan ta tafi makarantar firamare ta Waka inda ta kammala karatun Firamare a shekarar 1960.

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

Tsakanin 1961 da 1965, ta halarci makarantar sakandaren 'yan mata ta Dala, a Kano. Bayan haka, ta yi aiki a takaice a Bankin Barclays da Hukumar Tallace-tallace ta Arewacin Najeriya tsakanin 1966 da 1969. A watan Oktoba 1969, ta sami shiga Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) Zariya, inda ta samu difiloma a kan Doka a 1971. Tsakanin 1971 da 1972, ta yayi aiki a takaice a matsayin Mataimakiyar Magatakarda tare da Babbar Kotun Adalci ta Yankin Arewa Maso Gabas.

Ta fara karatun ta na Digiri na Lauya a ABU a 1972 kuma ta kammala cikin nasara a shekarar 1975. Daga nan ne Mai Shari’a Ogunbiyi ta zarce zuwa Makarantar Koyon Lauyoyi ta Nijeriya da ke Legas sannan aka kira ta zuwa Lauyan Najeriya a ranar 3 ga Yulin 1976.

A shekarar 1978, ta zarce zuwa Jami’ar Hull da ke Kasar Ingila inda ta samu Digiri na biyu a fannin Laifi. Ta kuma halarci ci gaba da karatun kwasa-kwasan ilimin shari'a a Cibiyar Nazarin Harkokin Shari'a ta Najeriya a Legas, a cikin 1985.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]