Edema Fuludu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Edema Fuludu
Ɗan Adam
Bayanai
Jinsi namiji
Shekarun haihuwa 8 Mayu 1970
Wurin haihuwa Burutu
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Matsayin daya buga/kware a ƙungiya Mai buga tsakiya
Mamba na ƙungiyar wasanni Ƙungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya
Wasa ƙwallon ƙafa

Edema Godmin Fuludu (an haife shi a ranar 8 ga watan Mayun 1970) tsohon ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne na Najeriya wanda ya taka leda a matsayin ɗan wasan tsakiya. Ya buga ƙwallo a kulob ɗin New Nigerian Bank da BCC Lions da Julius Berger da ke Najeriya da Altay a Turkiyya, sannan ya buga wa tawagar ƙwallon ƙafar Najeriya wasa a ƙasashen duniya.[1] Ya kasance cikin tawagar ƴan wasan Najeriya a gasar cin kofin nahiyar Afirka a shekarar 1994.[2] Fuludu ya yi aiki a matsayin kocin Warri Wolves.[3]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]