Gidan Telebijin na AIT

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Gidan Telebijin na AIT
Bayanai
Suna a hukumance
Africa Independent Television
Iri broadcast network (en) Fassara
Masana'anta broadcast network (en) Fassara
Ƙasa Najeriya
Aiki
Bangare na television in Nigeria (en) Fassara
Ƙaramar kamfani na
Harshen amfani Turanci
Mulki
Hedkwata Abuja
Mamallaki Africa Independent Television
ait.live

Gidan Talabiji mai zaman kansa na Africa, wanda kuma aka fi sani da AIT, gidan talabijin ne mai zaman kansa a Najeriya. Yana aiki da Yancin Watsa Labarai a Najeriya a matsayin babbar hanyar sadarwa ta talabijin mai zaman kanta[1] mai aiki da tashoshi a cikin jihohi ashirin da hudu daga cikin talatin da shida a Najeriya. Ana kuma haska tashar AIT ta satelite daga hedkwatarta da ke Abuja.[2] AIT wani reshe ne na DAAR Communications plc, ana samunsa a duk faɗin Afirka, kuma ta kafar sadarwa na Dish har zuwa Arewacin Amurka.

A cikin Ƙasar Ingila da Ireland, ana iya kama tashar akan tashar Sky 454 a matsayin tasha ta kyauta (asali ana biyan kuɗi kafin samun daman kallon tasharkafin zuwa 1 Agusta 2016). Akwai wani karin tashar da ake kira AIT Movistar, wanda ke kan tashar Sky 330, ya daina watsa shirye-shirye a kan 28 Yuli 2009. AIT International ta daina watsa shirye-shirye a Burtaniya da Ireland a ranar 15 ga Oktoba 2019.

Rufewa[gyara sashe | gyara masomin]

Wanda ya kafa gidan telebijin din wato Raymond Dokpesi ya jagoranci zanga-zangar lumana zuwa Majalisar Dokoki ta kasa a ranar 6 ga Yuni 2019 don gabatar da koke na neman sake duba dokokin watsa labarai.[ana buƙatar hujja]Raymond ya zanta da manema labarai da farko ya kira hankalin ‘yan jarida kan tsoma baki ta hanyar rubuce-rubuce, barazanar takunkumi da kuma son zuciya daga Darakta Janar, Modibbo Kawu[3] na Hukumar Yada Labarai ta Kasa (NBC), wanda ya kwanan nan ya fafata zaben fidda gwani a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar All Progressives Congress mai mulki a jihar Kwara . Dokpesi ya kuma yi zargin cewa hukumar ta NBC na aiki ne da umarnin fadar shugaban Najeriyar na dakile ayyukan gidan talabijin din a bisa zargin karya ka’idar yada labarai.

Hukumar kula da harkokin yada labarai ta kasa ta dakatar da lasisin watsa shirye-shiryen gidan talabijin na har abada a ranar 6 ga watan Yunin 2019 bisa dalilin rashin biyan kudin lasisi da kuma amfani da labarai da ke janyo tashin hankali a shafukan sada zumunta . [4]

Sai dai wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin sake bude gidan talabijin din a ranar 7 ga watan Yunin 2019. [5] [6]

Mutane[gyara sashe | gyara masomin]

  • Ohimi Amaize

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

  • Jerin gidajen talabijin a Najeriya

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Atiku, Shehu Sani, others speak on closure of AIT, Ray Power". Premium Times. Retrieved 8 December 2019.
  2. "Broadcast organisations". National Broadcasting Commission. Retrieved 23 December 2018.
  3. "Broadcast Regulator V Africa Independent Television (AIT)". Vanguard News. 9 June 2019. Retrieved 1 March 2022.
  4. NBC suspends AIT, Raypower's licenses indefinitely https://punchng.com/just-in-nbc-suspends-ait-raypowers-licences-indefinitely/amp/
  5. Court orders reopening of AIT, Raypower. https://www.premiumtimesng.com/news/headlines/333863-court-orders-reopening-of-ait-ray-power.html
  6. Court orders reopening of AIT, Raypower https://www.thecable.ng/just-in-court-orders-reopening-of-ait-raypower

Hanyoyin haɗi na waje[gyara sashe | gyara masomin]