Hamza Abdi Idleh[1] (an haife shi a ranar 16 ga watan Disambar 1991), ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne na Djibouti wanda ke taka leda a matsayin ɗan wasan tsakiya ga FC Dikhil/SGDT da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Djibouti .
Hamza ya fara karawa ne a ranar 22 ga watan Maris ɗin 2017, a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin Afrika ta shekarar 2019, ya kuma ci kwallonsa ta farko a kan Sudan ta Kudu da ci 2-0. A ranar 4 ga watan Satumbar 2019, ya bayyana a gasar neman cancantar shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2022 kuma ya zura kwallo ta biyu a kan Eswatini a ci 2-1.