Jump to content

Ibrahim Abubakar Njodi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ibrahim Abubakar Njodi
Rayuwa
Haihuwa Kaltungo
ƙasa Najeriya
Sana'a
Sana'a Malami da mataimakin shugaban jami'a

Ibrahim Abubakar Njodi (an haife shi a watan Janairu a shekara ta alif dari tara da hamsin da tara (1959). [1] Farfesa ne aɓangaren ilimin kiwon lafiya, ɗan Najeriya kuma tsohon mataimakin shugaban jami'ar Maiduguri.[2][3][4] Gwamna Inuwa Yahya ya naɗa Farfesa Ibrahim Njodi a matsayin sakataren gwamnatin jihar Gombe nan da nan bayan wa’adinsa ya cika a matsayin mataimakin shugaban jami’ar Maiduguri.[5]

Ibrahim Abubakar Njodi ya yi makarantar firamare ta L.E.A da ke Kaltungo daga 1967 zuwa 1973, sannan ya yi makarantar firamare ta ECWA a Kaltungo daga 1973 zuwa 1975. Daga 1975 zuwa 1980 ya halarci kwalejin malaman gwamnati da ke Jama’are a jihar Bauchi. Ya yi digirinsa na farko a fannin lafiya acikin shekarar ta 1985, daga Jami’ar Maiduguri. Daga baya, daga 1988 zuwa 1991, ya yi digirinsa na biyu a fannin ilmin kiwon lafiya a wannan jami'a. Daga 2000 zuwa 2003, ya yi karatun Ph.D. a fannin ilimin kiwon lafiyar jama'a a shahararriyar jami'ar Najeriya, Nsukka.[6][7]

Ya shiga aikin gwamnati ne a matsayin graduate assistant a Jami’ar Maiduguri a shekarar 1987. Njodi ya rike mukamin shugaban tsangayar ilimi na jami'ar daga 2008 zuwa 2010, sannan ya zamo Mataimakin Shugaban Jami'ar daga Yuni 2014 zuwa Yuni 2019.[8][6] A halin yanzu Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi shine sakataren gwamnatin jihar Gombe (SSG) na jihar Gombe.[9]