Khalida Zahir

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Khalida Zahir
Rayuwa
Haihuwa Omdurman, 18 ga Janairu, 1927
ƙasa Sudan
Mutuwa 9 ga Yuni, 2015
Karatu
Makaranta Faculty of Medicine University of Khartoum (en) Fassara
Sana'a
Sana'a likita da Mai kare hakkin mata
Mamba Sudanese Women's Union (en) Fassara

Khalida Zahir (Larabci: خالدة زاهر‎; 1927–2015, wanda kuma aka rubuta Khalda Zahir), ta kasance ɗaya daga cikin likitocin Sudan mata na farko kuma mai fafutukar kare hakkin mata.

Ƙuruciya da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Zahir a Omdurman. Ta kammala karatu daga Makarantar Magunguna ta Kitchener, wacce daga baya ta zama Jami'ar Khartoum, a shekara ta 1952, tare da Z Serkisiani.[1]

Aikin likita[gyara sashe | gyara masomin]

Khalida da Serkisiani su ne likitoci mata na farko a Sudan.[1]

Khalida ta yi wa talakawa kyauta a asibitinta. Ta zama shugabar kula da lafiyar yara a ma'aikatar lafiya ta Sudan. Ta yi ritaya a shekarar 1986.[2]

Harkar siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Khalida ita ce mace ta farko a cikin kungiyar ɗalibai a shekarar 1947 kuma ta shiga tattaunawar zaman lafiya dangane da kudancin Sudan a wannan shekarar. Khalida ta kasance ɗaya daga cikin mata kalilan da suka shiga jam’iyyar siyasa a shekarun 1940. Ta kafa kungiyar al'adu ta matasa tare da Fatima Talib a shekara ta 1948.[3] Kungiyar mata ta Sudan ta farko, ta ba da ilimi ga mata kan kiwon lafiya, karatu da rubutu.[2] Ta kasance cikin waɗanda suka kafa kungiyar mata ta Sudan (SWU) a shekarar 1952, kungiyar da ta yi fafutukar neman zaɓe da yancin aiki.[2] An zaɓi Khalida shugabar SWU a shekarar 1958.[4]

Mutuwa[gyara sashe | gyara masomin]

Khalida ta rasu ranar 9 ga watan Yuni 2015.[4]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 Mohamed IN, Abdelraheem MB, Abdullah MA (2012). "Sudanese female doctors in paediatrics" (PDF). Sudanese Journal of Paediatrics. 12 (2): 36–43. PMC 4949896. PMID 27493343.
  2. 2.0 2.1 2.2 Mubarak, Khalid Al (2015-06-23). "Khalida Zahir obituary". The Guardian (in Turanci). ISSN 0261-3077. Retrieved 2016-11-20.
  3. Turshen, Meredeth (2000-01-01). African Women's Health (in Turanci). Africa World Press. pp. xi. ISBN 9780865438125 – via Google Books.
  4. 4.0 4.1 Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named Sudanow_women_role_indep