Kisan kiyashin Dankade

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdevenimentKisan kiyashin Dankade
Iri Kisan Kiyashi
Bangare na Ƴan ƙungiyar fashi a Najeriya
Kwanan watan 14 –  15 ga Janairu, 2022
Wuri Kebbi
Ƙasa Najeriya
Adadin waɗanda suka rasu 18

A tsakiyar watan Janairun 2022, wasu gungun ƴan bindiga sun kashe sama da mutane 50 a Dankade, [lower-alpha 1] Jihar Kebbi, Najeriya.[1]

Matashiya[gyara sashe | gyara masomin]

Rikicin ‘yan fashin Najeriya ya faro ne tun a shekarar 2011, kuma ya fi faruwa a arewa maso yammacin Najeriya.[1] Ƙungiyoyin da ke ɗauke da muggan makamai sun kai hare-hare da dama da suka haɗa da garkuwa da jama’a da fashi da makami da kuma harbe-harbe. An kuma kashe ɗaruruwan mutane tare da raba dubbai da muhallansu. Rikicin ya ƙaru a farkon 2020s; Babban lamari kuma mafi muni shi ne kisan kiyashin da aka yi a jihar Zamfara a farkon watan Janairun shekarar 2022. Hukumomin Najeriya da ke adawa da ta'addancin Boko Haram da tashe- tashen hankula a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya na fuskantar matsalar 'yan ta'addar.

Lamarin[gyara sashe | gyara masomin]

Da yammacin ranar 14 ga watan Janairun shekarar 2022, wasu gungun ‘yan bindiga sun kai hari a ƙauyen Dankade a jihar Kebbi a arewa maso yammacin Najeriya.[1] Bayan harbi da aka yi da sojoji da ‘yan sanda inda sojoji biyu da dan sanda guda suka mutu, jami’an tsaro sun ja da baya.[1] Ƴan ƙungiyar sun ci gaba da kai hare-hare tun washegari, inda suka kashe mazauna ƙauyukan da dama, da kona shaguna da hatsi, da kuma sace-sacen shanu.[2] Ƙungiyar kuma ta yi garkuwa da wasu mutanen ƙauyen, ciki har da shugaban wannan al'umma. [1] A lokacin da ‘yan fashin suka bar ƙauyen Dankade ɗin sun bar gawarwaki birjik a kan titunan garin.[3]

Wani wanda ya tsira ya iya tuna cewar:

“An kashe da dama kuma an kona gawarwakinsu. Ba za mu iya tantance adadin wadanda suka mutu ba a yanzu. An bar mu muna mamakin dalilin da ya kuma sa ake ganin kashe-kashen ta’addanci na ƙaruwa, musamman a yankin Arewa maso Yamma.”[4]

Hukumomin jihar sun ce adadin waɗanda suka mutu ya kai 18, yayin da wasu mazauna yankin suka ce ‘yan bindigar sun kashe fararen hula sama da 50.[5]

Bayanan kula[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Alternatively spelled Dan-Kade.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 1.2 1.3 1.4 Muhammad, Garba (2022-01-16). "Gunmen kill more than 50 in Nigeria's northwest, residents say". Reuters (in Turanci). Retrieved 2022-01-19.
  2. "West and Central Africa: Weekly Regional Humanitarian Snapshot (11-17 January 2022) - Nigeria". ReliefWeb (in Turanci). Retrieved 2022-01-19.
  3. "Gunmen kill more than 50 in Nigeria's northwest, residents say". euronews (in Turanci). 2022-01-17. Retrieved 2022-01-19.
  4. "JUST IN: Scores feared dead as gunmen attack Kebbi community, burn corpses". Punch Newspapers (in Turanci). 2022-01-17. Retrieved 2022-01-19.
  5. "Bandits kill 16, abduct many in Kebbi". Vanguard News (in Turanci). 2022-01-17. Retrieved 2022-01-19.