Masarautar Say

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Masarautar Say
Emirate (en) Fassara
Bayanai
Addini Musulunci
Wanda ya samar Alfa Mohamed Diobo (en) Fassara
Babban birni Say (gari)

Masarautar Say wata daular Musulunci ce ta kafa a 1825 da Alfa Mohamed Diobo, shugaban Sufaye na Qadiriyya wanda ya zo Say daga Djenné (Mali) a shekarar 1810. Duk da cewa Diobo ba mai nasara ba ne, amma ikonsa a kan Say ya tabbata daga sanannun malamansa da kuma kariya ta diflomasiya na Daular Sakkwato, wanda wani malami bafulatani Sufi na Kadiriyya, Usman Dan Fodio ya kafa.

A zamaninta, Masarautar Say ta shahara tun daga Gao har zuwa Gaya a matsayin cibiyar ilmantarwa da takawa. Ana kyautata zaton cewa a lokaci guda tana da mazauna 30,000 kuma ta kaddamar da nata ayarin ƙetare na sahara. Birnin Say ya ci gaba da rike gwamnatin gargajiya da zuriyar Diobo ke rike da ita a ofishin "al/aize" (a zahiri, dan liman, ne a zarma). Sune kamar haka; Alfa Mohamed Diobo (1825—1834), Boubacar Modibo (1834–1860), Abdourahman (1860–1872), Moulaye (1872–1874), Abdoulwahidou (1874–1878), Saliha Alfa Baba (1878–1885), Amau Moudi (1885-1893), Halirou Abdoulwahabi (1893-1894).[1] [2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Idrissa, Abdourahmane; Decalo, Samuel (2012), Historical Dictionary of Niger by Abdourahmane Idrissa, Samuel Decalo, Page 399 , ISBN 9780810870901 , retrieved 2021-03-18
  2. Seeda (2014), Qui est Alpha Mahaman Diobbo ? , Niamey.com, retrieved 2021-03-18