Mohammed Bagayogo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Mohammed Bagayogo
Rayuwa
Haihuwa Djenné, 1523 (Gregorian)
ƙasa Daular Mali
Mutuwa Timbuktu, 7 ga Yuli, 1593
Sana'a
Sana'a marubuci da mai falsafa

Mohammed Bagayogo Es Sudane Al Wangari Al Timbukti fitaccen malami ne daga Timbuktu, Mali. Shi ne Sheik kuma farfesa na babban malami, Ahmed Baba kuma malami a Madrasah ta Sankore, ɗaya daga cikin makarantun falsafa uku a ƙasar Mali a lokacin zamanin zinare na yammacin Afirka (Golden age) (watau ƙarni na 12-16); sauran biyun kuma su ne Masallacin Sidi Yahya da Masallacin Djinguereber.[1] An haife shi a Djenné a shekara ta 1523. An adana adadi mai yawa na rubuce-rubucen da ya rubuta a cikin rubutun hannu a Cibiyar Ahmed Baba, wurin ajiyar adabin Afirka. Wasu daga cikin rubuce-rubucen sun sami hanyar shiga gidajen tarihi na Faransa.[2] Ana ci gaba da gudanar da wani aiki na ƙirƙirar waɗannan rubuce-rubucen da za su haifar da ƙarin fahimtar al'adun da suka bunƙasa a Mali a zamanin da.[3]

Mohammed Bagayogo shi ma yana da matsayi a tarihin Mali saboda kin bin umarnin 'yan mamaya na Moroko.[4] Ya rasu a ranar 7 ga watan Yuli, 1593, a wani tsohon garin Timbuktu a yanzu.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Adama, Hamadou. "Ahmed Bâba at-Timbuktî." In Oxford Research Encyclopedia of African History. 2021.
  2. Hunwick, John. "Timbuktu: A Refuge of Scholarly and Righteous Folk." Sudanic Africa14 (2003): 13-20.
  3. Hunwick, John. "Towards a History of the Islamic Intellectual Tradition in West Africa down to the Nineteenth Century." Journal for Islamic Studies 17 (1997): 4.
  4. "History of Timbuktu, Mali". Archived from the original on July 4, 2007. Retrieved 2007-07-17.