Jump to content

Moses Armah

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Moses Armah
Rayuwa
Sana'a
Sana'a ɗan kasuwa

Moses Armah 'Parker' Dan kasuwa ne dan kasar Ghana, mai kula da kwallon kafa kuma a halin yanzu shi ne mai kula da shugabancin Medeama SC da kuma shugaban rukunin kamfanonin Mospacka wanda ya hada da Medeama FM.[1]

A watan Yulin na shekara ta 2010, dan kasuwar ya kammala karbe ikon Kessben FC akan kudi dalar Amurka 600,000 kuma ya sake mata suna Medeama SC. [2]

A yayin babban zaben kungiyar kwallon kafa ta Ghana na shekara ta 2019 Moses Armah ya wakilci Medeama SC a matsayin wakili kuma ya kada kuri'a a madadin kungiyar.[3]

Kafofin yada labarai na Ghana da dama sun ruwaito cewa yana da hannu a rikicin da tsohon dan wasan tsakiya na AC Milan Sulley Ali Muntari a lokacin gasar cin kofin duniya na FIFA a shekara ta 2014 da Ghana ta buga a Brazil.[4] A halin da ake ciki, a wata hira da gidan rediyon Ghana Happy FM Moses Armah a shekarar 2016 ya ce ya yafewa Muntari kan lamarin.[5] An kora Muntari zuwa gida da wuri daga sansanin Ghana tare da Kevin-Prince Boateng saboda lamarin. [6] Tsohon kocin Ghana James Kwesi Appiah ya bayyana cikakken bayani game da lamarin a littafinsa mai suna Leaders Don't have to Yell. [7]

Bayan samun Medeama a shekara ta 2010 Moses Armah ya ci gaba da daukaka martabar kulob din yayin da ya wakilci Ghana sau biyu a gasar kungiyoyin kwallon kafa ta Afirka ta hanyar taka leda a gasar cin kofin CAF Confederation a shekarun 2014 da 2016.[8][9]

Ya kuafa Wassaman FC wanda a watan Yuli 2013 aka canza mata suna zuwa Emmanuel Stars FC kuma Fasto TB Joshua ya siye ta.

Girmamawa[gyara sashe | gyara masomin]

A watan Nuwamba 2018 aka karrama Moses Armah a kasar Canada saboda gudunmawar da ya bayar wajen bunkasa kwallon kafa a yammacin Afrika.[10]

Ya jagoranci Medeama SC don doke Asante Kotoko don lashe Kofin FA na Ghana a shekarar 2015.[11] Hakan ya biyo bayan irin nasarar da aka samu a kan wannan bangaren Kotoko shekaru biyu da suka gabata.[12]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Medeama president Moses Armah receives top award in Canada" . GhanaSoccernet . 27 November 2018. Retrieved 2020-07-07.
  2. "Find out how corrupt referees compelled team owner to sell the club – Ghana Sports Online" . 16 September 2019. Retrieved 2020-07-07.
  3. "Premier League clubs submit names to vote at GFA Elective Congress" . www.ghanaweb.com . 2019-10-15. Retrieved 2020-07-07.
  4. "Why Muntari slapped Moses Armah - Nyantakyi" . Graphic Online . Retrieved 2020-07-07.
  5. "Moses Armah 'Parker' finally opens up on Muntari feud" . www.ghanaweb.com . 2016-06-22. Retrieved 2020-07-07.
  6. "Boateng, Muntari sent home, suspended 'indefinitely' by Ghana" . Eurosport . 2014-06-26. Retrieved 2020-07-07.
  7. "Ex-Ghana coach Kwesi Appiah reveals Sulley Muntari bruises with blood after 2014 World Cup fight" . GhanaSoccernet . 4 February 2020. Retrieved 2020-07-07.
  8. Association, Ghana Football. "Medeama drawn in Group A of CAF Confederations Cup" . www.ghanafa.org . Retrieved 2020-07-07.
  9. "Medeama SC through to play-off round of Caf Confederation Cup after 2-1 aggregate win over Zesco United | Goal.com" . www.goal.com . Retrieved 2020-07-07.
  10. "Medeama president Moses Armah receives top award in Canada" . GhanaSoccernet . 27 November 2018. Retrieved 2020-07-07.
  11. "FA Cup Final: Medeama beats Asante Kotoko 2-1" . www.ghanaweb.com . 2015-08-30. Retrieved 2020-07-07.
  12. "Medeama stun Kotoko to win FA Cup" . Pulse Gh . 2016-08-30. Retrieved 2020-07-07.