Novatus Dismas
|
| |||||||||||||||||||||||
| Rayuwa | |||||||||||||||||||||||
| Haihuwa |
Tanga, Tanzania da Arusha (mul) | ||||||||||||||||||||||
| ƙasa | Tanzaniya | ||||||||||||||||||||||
| Karatu | |||||||||||||||||||||||
| Harsuna | Turanci | ||||||||||||||||||||||
| Sana'a | |||||||||||||||||||||||
| Sana'a | ɗan wasan ƙwallon ƙafa | ||||||||||||||||||||||
| |||||||||||||||||||||||
| Tsayi | 185 cm | ||||||||||||||||||||||
Novatus Dismas Miroshi (an haife shi ranar 2 ga watan Satumba, 2002), ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne ɗan ƙasar Tanzaniya wanda ke taka leda a ƙungiyar ƙasa ta Tanzaniya.[1]
Ya buga wasan kasa da kasa tare da tawagar 'yan kasa da shekaru 20 ta Tanzaniya a ranar 16 ga Fabrairu 2021 da Ghana da ke fafatawa a gasar cin kofin Afrika na 'yan kasa da shekaru 20 da aka yi a Mauritania a ci 4-0.[2]
A ranar 19 ga watan Fabrairu, 2021, Dismas ya ci wa Tanzania kwallonsa ta farko a ragar Gambia a wasan da suka tashi 1-1.[3]
A ranar 2 ga watan Satumba 2021, ya fara buga babban wasansa na farko da Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA a 2022 a kunnen doki 1-1.[4]
A ranar 7 ga watan Satumba, 2021, Dismas ya ci wa Tanzania babbar kwallo ta farko a ragar Madagascar a wasan neman tikitin shiga gasar da ci 3-2.[5]
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]- ↑ "Tanzania-N. Dismas Miroshi - Profile with news, career statistics and history - Soccerway". us.soccerway.com . Retrieved 2021-09-11.
- ↑ "Tanzania-N. Dismas Miroshi-Profile with news, career statistics and history - Soccerway". us.soccerway.com . Retrieved 2021-09-11.
- ↑ Tanzania-N. Dismas Miroshi-Profile with news, career statistics and history - Soccerway". us.soccerway.com . Retrieved 2021-09-11.
- ↑ "FIFA". fifa.com. Retrieved 2021-09-11.
- ↑ "FIFA". fifa.com. Retrieved 2021-09-11.