Rashid Seidu

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Rashid Seidu
Rayuwa
Haihuwa Accra, 14 Satumba 1995 (28 shekaru)
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
Asante Kotoko F.C. (en) Fassara-
 

Rashid Seidu (an haife shi a ranar 14 ga watan Satumban 1995) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne, ɗan ƙasar Ghana wanda ke taka leda a matsayin mai tsaron gida. A cikin shekarar 2015, ya sami kira na ƙasa kuma ya kasance memba na Ghana U23 a 2015 All-Africa Games. [1]

Aikin kulob[gyara sashe | gyara masomin]

Seidu ya rattaba hannu a ƙungiyar ƙwararru ta Asante Kotoko, a ranar 3 ga watan Janairun 2011. Kuma ya koma kulob ɗin AS Douanes na Nijar (Niger) inda ya ƙulla kwantiragi na shekara tare da zaɓin sabunta shi a ƙarshen kakar wasa ta bana amma ya ɗan yi jinkiri[2].

Daga bisani ya koma Bechem United a cikin watan Yulin 2013, inda ya rattaɓa hannu kan shekaru biyu da kulob ɗin gasar Premier ta Ghana[3][4].

A cikin shekarar 2015, Seidu ya koma kulob ɗin gasar Premier ta Ghana Wa All Stars yanzu Legon Cities kan yarjejeniyar shekaru huɗu. A cikin watan Mayun 2020, ya shiga Inter Allies.

Ayyukan ƙasa da ƙasa[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin watan Janairun 2015 an gayyace shi don shiga cikin tawagar ƙasa ta U23 a wasannin share fage na Wasannin Afirka duka.

Girmamawa[gyara sashe | gyara masomin]

Kulob[gyara sashe | gyara masomin]

Asante Kotoko

  • Gana Premier League: 2011-2012

Bechem United

Wa All Stars

  • Gana Premier League: 2016
  • Gana Super Cup: 2017

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

Hanyoyin haɗi na waje[gyara sashe | gyara masomin]

  • Rashid Seidu at FootballDatabase.eu