Rikicin Sudan, 2023

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdevenimentRikicin Sudan, 2023

Iri attempted coup d'état (en) Fassara
civil war (en) Fassara
rikici
Bangare na 2019 Sudanese transition to democracy (en) Fassara
Kwanan watan 2023
Wuri Khartoum
Ƙasa Sudan
Participant (en) Fassara
Adadin waɗanda suka rasu 413 (a data de 22 ga Afirilu, 2023)
Adadin waɗanda suka samu raunuka 3,000 (a data de 19 ga Afirilu, 2023)
Hanyar isar da saƙo
Has part(s) (en) Fassara
timeline of the 2023 Sudan conflict (en) Fassara
Operation Raus aus Khartum (en) Fassara

A ranar 15 ga watan Afrilu, 2023, rikici ya ɓarke a fadin kasar Sudan, musamman a babban birnin ƙasar Khartoum da yankin Darfur, tsakanin ɓangarorin gwamnatin mulkin sojan kasar. Ya zuwa ranar 20 ga watan Afrilu, kusan mutane 330 ne aka kashe kuma kusan 3,200 suka jikkata.[1]

Faɗan dai ya fara ne da hare-haren da dakarun Rapid Support Forces (RSF) suka kai kan muhimman wuraren gwamnati. An kai hare-hare ta sama da manya-manyan bindigogi a duk fadin kasar ta Sudan ciki har da Khartoum babban birnin ƙasar. Ya zuwa ranar 15 ga watan Afrilu, 2023 Shugaban RSF Mohamed Hamdan Dagalo da shugaban Sudan Abdel Fattah al-Burhan sun yi iƙirarin cewa suna riƙe da muhimman wuraren gwamnati da suka haɗa da babban ofishin sojoji, fadar shugaban kasa, filin jirgin sama na Khartoum, ofishin babban hafsan soji da kuma hedkwatar Sudan TV ta Sudan.[2][3][4][5]

Wai-wa-ye[gyara sashe | gyara masomin]

A Tarihin rikice-rikice a Sudan ya ƙunshi rikice-rikice na kabilanci, rikice-rikice na addini, da gasa kan albarkatun ƙasar. [6] [7] A cikin tarihin zamanin nan, yakin basasa guda biyu tsakanin gwamnatin tsakiya da yankunan kudancin kasar ya kashe mutane miliyan 1.5, kuma rikicin da ake ci gaba da yi a yankin yammacin Darfur ya yi sanadin raba mutane miliyan biyu da muhallansu tare da kashe sama da mutane 200,000. Tun bayan samun ‘yancin kai a shekarar 1956, Sudan ta yi juyin mulkin soja sama da goma sha biyar kuma sojoji ne ke mulki a mafi yawan wanzuwar wuraren jamhuriyar ƙasar, tare da ɗan kankanen lokaci na mulkin farar hula na majalisar dokoki.

Yanayin siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://www.aljazeera.com/news/liveblog/2023/4/20/sudan-live-news-ceasefire-falters-as-nearly-300-killed
  2. https://www.bbc.com/news/world-africa-65284945
  3. "At least 25 killed, 183 injured in ongoing clashes across Sudan as paramilitary group claims control of presidential palace". CNN. 15 April 2023. Archived from the original on 17 April 2023. Retrieved 15 April 2023.
  4. Mullany, Gerry (15 April 2023). "Sudan Erupts in Chaos: Who Is Battling for Control and Why It Matters". The New York Times. Archived from the original on 15 April 2023. Retrieved 15 April 2023.
  5. Akinwotu, Emmanuel (15 April 2023). "Gunfire and explosions erupt across Sudan's capital as military rivals clash". Lagos, Nigeria: NPR. Archived from the original on 15 April 2023. Retrieved 15 April 2023.
  6. Empty citation (help)
  7. Empty citation (help)