Suratul Maryam

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Suratul Maryam
Surah
Bayanai
Bangare na Al Kur'ani
Suna saboda Maryam a Musulunci
Akwai nau'insa ko fassara Maryam da Maryam
Harshen aiki ko suna Larabci
Full work available at URL (en) Fassara quran.com…
Has characteristic (en) Fassara Surorin Makka

Suratul Maryam (Larabci: مريم‎, Maryam ; Larabci ma'anar "Maryama") ita ce surah ta goma sha tara (19)(sūrah) Acikin Al-Qur'ani mai girma ayoyinta 98 (āyāt). Dukkanin surori 114 na cikin Al-Qur'ani an tsara sune daidai da tsarin da aka bi tun lokacin Khalifa Usman. An sanyawa ita wannan surah ta Al-Qur'ani mai girma suna Maryam ne saboda a cikinta an bada labarin Maryamu, mahaifiyar Annabi Isah (Yesu) alaihis salam. A cikinta an ba da labarin abubuwan da suka faru kafin haihuwar Yesu, batun da ke cikin Luka 1 na Baibul ɗin Kirista. Ayoyin cikin surar sun yi bada labaran sanannun annabawa da yawa, wanda suka haɗa da Ishaku, Yakubu, Musa, Haruna, Isma'il, Idris, Adam, da Nuhu.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]