Tokunbo Afikuyomi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Tokunbo Afikuyomi
Ɗan Adam
Bayanai
Bangare na Nigerian senators of the 4th National Assembly (en) Fassara da Nigerian senators of the 5th National Assembly (en) Fassara
Jinsi namiji
Ƙasar asali Najeriya
Wurin haihuwa Lagos
Sana'a ɗan siyasa
Muƙamin da ya riƙe mamba a majalisar dattijai ta Najeriya da mamba a majalisar dattijai ta Najeriya
Ɗan bangaren siyasa Alliance for Democracy (en) Fassara

Tokunbo Afikuyomi (An haife shi a shekara ta 1962) ɗan siyasar Najeriya ne, wanda aka zaɓe shi Sanata mai wakiltar mazaɓar Legas ta tsakiya a farkon jamhuriya ta huɗu ta Najeriya, ya yi takara a dandalin jam'iyyar Alliance for Democracy (AD). Ya hau mulki a cikin watan Yunin 1999.[1] Ya sauya sheƙa a cikin watan Afrilun shekarata 2002, ya kuma tsaya takarar jam’iyyar AD a mazaɓar Legas ta Yamma, bayan Sanata Wahab Dosunmu ya koma jam'iyyar PDP.[2]

An haifi Afikuyomi a shekara ta 1962, kuma ya sami digiri na B.Sc. Ya kasance mamba a majalisar wakilai kuma mataimaki na musamman ga shugaban jam'iyyar Social Democratic Party (SDP) na ƙasa a lokacin da jamhuriya ta uku ta soke Najeriya.[3][4] Bayan ya hau kujerar majalisar dattawa a cikin watan Yunin shekarar 1999, an naɗa Afikuyomi a kwamitocin harkokin sufurin jiragen sama, harkokin ƙasashen waje, harkokin mata, asusun gwamnati da kuma halin tarayya.[5] Babatunde Fashola ne ya naɗa Afikuyomi kwamishinan yawon buɗe ido a jihar Legas a wa’adinsa na farko na gwamna.[6]

A shekarar 2017, Sanata Afikuyomi shi ne shugaban kwamitin zaɓen jam’iyyar APC na jiha.[7]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]