Binta Mamman

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Binta Mamman
House of Assembly (en) Fassara

Rayuwa
Haihuwa Jihar Neja
ƙasa Najeriya
Karatu
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da administrator (en) Fassara
Imani
Jam'iyar siyasa All Progressives Congress

Binta Mamman ƴar siyasa ce daga jihar Neja dake Najeriya. Ta kammala karatun ta na Business Administration. Kafin ta shiga siyasa ta kasance matar gida.[1]

Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Mamman ta fara siyasarta ne a jam’iyyar PDP a cikin shekarar 2015, inda ta samu zama mamba mai wakiltar Gurara, a majalisar dokokin jihar Neja, kuma ta sake tsayawa takara a shekarar 2019 ƙarƙashin jam’iyyar APC.[2]

A halin yanzu dai Mamman ita ce mace ɗaya tilo a majalisar dokokin jihar Neja mai wakiltar mazaɓar Gurara a ƙarƙashin jam’iyyar APC. Ita ce shugabar kwamitin majalisar dokokin jihar Neja mai kula da harkokin jinsi da ci gaban zamantakewa. An zaɓe ta a matsayin shugabar mata ta farko a NSHA.[1]

A shekarar 2017, ƙungiyar kare muhalli ta ƙasa da ƙasa ta ba ta lambar yabo a matsayin tambarin ci gaban al’umma a jihar Neja kuma a shekarar 2021 ta ɗauki nauyin ƙudirin doka kan cin zarafin mata da aka yi wa laƙabi da dokar hana cin zarafin jama’a ta jihar Neja wadda za ta daƙile ƙaruwar ƙararraki. na Tashe-tashen hankula masu nasaba da Jinsi a jihar.[3] Ta kuma gabatar da wani ƙudiri na hukuncin kisa ga masu fyaɗe a cikin shekarar 2020.[4]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 https://thenationonlineng.net/people-thought-i-was-wasting-my-time-niger-assembly-only-female-rep/
  2. https://sunnewsonline.com/niger-lawmakers-sack-house-leader-deputy/
  3. https://dailypost.ng/2020/06/18/niger-state-assembly-calls-for-death-penalty-for-rape-offenders/
  4. https://ngf.org.ng/index.php/99-news-from-the-states/2020-niger-state-governor-abubakar-sani-bello-signs-two-bills-into-law