Fareda Banda

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Fareda Banda
Rayuwa
Sana'a
Sana'a legal scholar (en) Fassara da Malami
Employers School of Oriental and African Studies, University of London (en) Fassara
Mamba Black Female Professors Forum (en) Fassara

Fareda Banda Malamar jami'ar ce 'yar ƙasar Zimbabwe. A halin yanzu ita farfesa ce a fannin shari'a a Jami'ar SOAS ta London.[1]

Tarihin Rayuwa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Fareda Banda kuma ta girma a ƙasar Zimbabwe.[2] Ta yi karatu a fannin shari'a a Jami'ar Zimbabwe, inda ta kammala a cikin manyan uku (top three).[1] Wannan ya kai ta ga samun nasarar Beit Fellowship zuwa Jami'ar Oxford, inda ta kammala digirinta na uku kan batun "samun adalci ga mata". Bayan kammala karatun digirinta, Banda ta yi aiki da Hukumar Shari'a ta Ingila ta Wales kafin ta koma Oxford a matsayin mai bincike na gaba da digiri.[1]

Ta kasance farfesa a Jami'ar SOAS ta London tun a shekarar 1996 a Makarantar Nazarin Gabas da Afirka. Manyan bangarorin aikinta sun haɗa da kare hakkin mata da dokokin iyali a Afirka.[3]

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Banda tsohuwar mai bincike ce tare da UNRISD inda ta yi aiki akan 'Kare Yancin Mata.[4]

Fareda Banda tayi aikin koyarwa a Jami'ar SOAS ta London, Banda kuma tana koyar da shirin bazara a Jami'ar Oxford kan 'yancin mata. Ta kuma koyar da shirye-shirye a faɗin duniya a garuruwan da suka haɗa da Harare, Kampala, Onati da Oslo.[4]

Banda ita ce marubuciyar 2022 littafin ƙaura na Afirka, Haƙƙin Ɗan Adam da Adabi.[5] A cikin shekarar 2023, ta kasance shugabar bada lambar yabo ta Caine da Rubutun Afirka.[6]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 1.2 "Professor Fareda Banda | Staff | SOAS University of London". www.soas.ac.uk (in Turanci). Retrieved 2022-02-10.
  2. "Professor Fareda Banda featured in Phhenomenal Women: Portraits of UK Black Female Professors". www.soas.ac.uk (in Turanci). 9 March 2020. Retrieved 15 October 2023.
  3. "Fareda Banda". www.amazon.co.uk (in Turanci). Retrieved 2022-02-10.
  4. 4.0 4.1 "Fareda Banda | Staff | About UNRISD | UNRISD". www.unrisd.org. Retrieved 2022-02-10.
  5. African Migration, Human Rights and Literature. Hart Publishing. ISBN 9781509945467.
  6. "'I Wanted to See if I Could Pull Off Writing an Interdisciplinary Book' | Fareda Banda's First Draft". The Republic. Nigeria. 6 October 2023. Retrieved 15 October 2023.