Folashade Adefisayo

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Folashade Adefisayo
Rayuwa
Haihuwa Lagos
ƙasa Najeriya
Karatu
Harsuna Turanci
Yarbanci
Sana'a
Sana'a Malami da commissioner (en) Fassara
Wurin aiki Lagos

Folashade Adefisayo Malama ce ƴar Najeriya ce kuma malama, kuma kwamishina a yanzu a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Legas[1][2][3][4].

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Ta halarci jami’ar Ibadan inda ta samu digiri na farko a fannin ilmin dabbobi . Daga baya ta koma Jami'ar Jihar Legas inda ta sami Digiri na biyu a kan Gudanar da Harkokin Kasuwanci sannan zuwa Jami'ar Nottingham ta sake samun wani digiri na biyu a fannin Ilimi.

Ayyuka[gyara sashe | gyara masomin]

Folashade ta shirya wani shiri domin inganta ɗalibai a Kwalejin Kwamfuta (CBT), bayan an kullen COVID-19 a cikin jihar Legas, an shirya shirin don inganta kimanin ɗalibai miliyon 1.5 a duk faɗin jihar Legas da Nijeriya. Ta kuma ba da umarnin a daukaka darajar daliban Legas zuwa aji na gaba ta hanyar la’akari da ci gaba da tantancewar (CA Test).

Rayuwar mutum[gyara sashe | gyara masomin]

Folashade an haife ta kuma ta girma a yankin Legas da Ibadan ,su biyar ne a danginsu. Ita ce diyar fari, kuma tana son karatu da balaguro.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Edugist Presents a Seasoned Academic, Folasade Adefisayo, to Proffer Ways to Revive and Strengthen Public Education in Nigeria". Edugist (in Turanci). 2019-01-13. Retrieved 2020-11-11.
  2. "Lagos orders resumption of remaining classes in public, private schools". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2020-10-13. Retrieved 2020-11-11.
  3. "Lagos is prepared for new normal in education —Adefisayo -". Vanguard News (in Turanci). 2020-08-06. Retrieved 2020-11-11.
  4. "Folashade Adefisayo Archives | Premium Times Nigeria" (in Turanci). Retrieved 2020-11-11.

Hanyoyin haɗin waje[gyara sashe | gyara masomin]

  • "Ministry of Education – Lagos State Government". education.lagosstate.gov.ng. Retrieved 2020-11-11.