Gérardine Mukeshimana

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Gérardine Mukeshimana
Minister of Agriculture and Animal Resources (en) Fassara

ga Yuli, 2014 - ga Maris, 2023
Rayuwa
Haihuwa Ruwanda, 10 Disamba 1970 (53 shekaru)
ƙasa Ruwanda
Mazauni Kigali
Karatu
Makaranta Michigan State University (en) Fassara
National University of Rwanda (en) Fassara
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Gérardine Mukeshimana masaniya ce a fannin kimiyya kuma 'yar siyasa ta ƙasar Rwanda wacce ta yi aiki a matsayin Ministar Noma da Albarkatun Dabbobi daga watan Yuli 2014[1] har zuwa ranar 2 ga watan Maris 2023.[2] An naɗa ta mataimakiyar shugabar asusun bunkasa noma ta duniya a watan Agustan 2023.[3]

Rayuwar farko da ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Mukeshimana a ranar 10 ga watan Disamba 1970 a gundumar Huye ta yau.[1] Tana da digiri a fannin Injiniyancin aikin gona daga Jami'ar Ƙasa ta Ruwanda da digiri na biyu (2001) da PhD (2013) a fannin ilimin halittu daga Jami'ar Jihar Michigan.[4][5] Kundin karatun digirinta yana da taken "Dissecting the Genetic Complexity of Drought Tolerance Mechanisms in Common Bean (Phaseolus Vulgaris L.)"[6] A cikin shekarar 2012, an ba ta lambar yabo ta 2012 don ci gaban Abinci da Aikin Noma na ƙasa (BIFAD) da Student Award for Science Excellence. don gudunmuwarta ga shirin noman wake na Rwanda.[6]

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Mukeshimana malama ce a tsangayar aikin gona a jami'ar ƙasa ta Rwanda kuma mai kula da ayyukan tallafawa yankunan karkara na bankin duniya.[6]

A cikin shekarar 2013, Mukeshimana tana cikin ƙungiyar bincike a BecA Hub, cibiyar nazarin halittu a Cibiyar Nazarin Dabbobi ta Duniya a Nairobi.[6]

Mukeshimana an naɗa ta Ministar Noma da Albarkatun Dabbobi a majalisar ministocin Firayim Minista Anastase Murekezi a watan Yulin 2014.[7][8] Ta ci gaba da riƙe muƙamin ta a wani sauyi a majalisar ministocin da shugaba Paul Kagame ya yi a watan Mayun 2016.[9]

A watan Yunin 2016, Mukeshimana ta karɓi bakuncin makon Kimiyyar Noma na Afirka karo na 7 da babban taron dandalin bincike kan aikin gona a Afirka (FARA) a Kigali, wacce ta gabatar da kira mai ɗauke da maki shida don cimma nasarar shirin "Ciyar da Afirka".[10] A cikin sauya shekar majalisar ministocin na 31 ga watan Agusta 2017, Mukeshimana ta ci gaba da riƙe muƙamin ta na majalisar ministoci da kuma kundin aikinta.[11]

Mukeshimana an naɗa ta mataimakiyar shugaban asusun bunkasa noma na ƙasa da ƙasa a watan Agustan 2023.[12]

Wallafe-wallafe[gyara sashe | gyara masomin]

  • Mukeshimana, Gerardine; Lasley, Amy L. (May 2014). "Identification of Shoot Traits Related to Drought Tolerance in Common Bean Seedlings". Journal of the American Society for Horticultural Science. American Society for Horticultural Science. 139 (3): 299–309. doi:10.21273/JASHS.139.3.299.
  • Mukeshimana, Gerardine; Butare, Louis; Cregan, Perry B.; Kelly, James D. (May 2014). "Quantitative Trait Loci Associated with Drought Tolerance in Common Bean". Crop Science. 54 (3): 923–938. doi:10.2135/cropsci2013.06.0427.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 Umutesi, Doreen (31 July 2014). "Meet the new female faces in cabinet". New Times (Rwanda). Kigali. Retrieved 1 September 2017.
  2. Daniel, Sabiiti (March 3, 2023). "Kagame Drops Agriculture Minister alongside the Shortest-serving Agriculture Board Director". KTpress.rw.
  3. "African leader Gerardine Mukeshimana joins UN rural development agency IFAD as Vice-President". IFAD (in Holanci). Retrieved 2023-09-08.
  4. Rwanda Today (26 December 2014). "Rwandans who will be the centre of focus in 2015". The East African. Retrieved 11 August 2017.
  5. "MINAGRI gets new ministers". Republic of Rwanda Ministry of Agriculture and Animal Resources. Archived from the original on 2017-08-11. Retrieved 2023-12-13.
  6. 6.0 6.1 6.2 6.3 Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named bourlag
  7. "Rwandan Ambassador to Nigeria returns as Sports Minister to Kigali". ATQ News. 2 August 2014. Retrieved 11 August 2017.
  8. "Habineza back at old portfolio and to host Kagame Cup in matter of days". Voice of Sport. 24 July 2014. Archived from the original on 11 August 2017. Retrieved 11 August 2017.
  9. Munyaneza, James (10 May 2016). "Rwanda: Kagame Shakes Up Cabinet, Names Three New Governors". The New Times. AfricaTime.com. Archived from the original on 11 August 2017. Retrieved 11 August 2017.
  10. "Agricultural Scientists Adopt Six-Point Call To Action To Feed Africa". The Herald. 22 June 2016. Archived from the original on 16 July 2019. Retrieved 11 August 2017.
  11. Kimenyi, Felly (31 August 2017). "Rwanda gets new Cabinet, who is in?". New Times (Rwanda). Kigali. Retrieved 1 September 2017.
  12. "African leader Gerardine Mukeshimana joins UN rural development agency IFAD as Vice-President". IFAD (in Holanci). Retrieved 2023-09-08.