Monsor Olowosago

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Monsor Olowosago
Rayuwa
Sana'a
Sana'a ɗan jarida

Monzor Olowosago ɗan jarida ne kuma mawallafin jaridar Oriwu Sun Community, da ke Ikorodu, ƙauyen mai tazarar kilomita 32 daga arewa maso gabas da Ikeja, babban birnin jihar Legas, cibiyar kasuwancin Najeriya. Jaridar ta shafe shekaru 36 tana wallafa labarai, ba tare da hutu ba, tun daga 1985, wanda hakan ya sa ta zama Jarida ta farko a Najeriya.[1]

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Monzor Olowosago a ranar 15 ga watan Mayu, 1951. Ya cika shekaru 70 a ranar 15 ga watan Mayu, 2021, kuma tsohon Shugaban Tarayyar Najeriya Muhammadu Buhari ya taya shi murna.[2][1] Ya shafe shekaru 36 yana buga labarai wa al'umma.

Monsor Olowosago ya halarci Kwalejin Aikin Jarida ta Landan. Yayin da yake Landan, ya zauna a Arewacin London. Zaman da ya yi a Arewacin Landan ya tayar da hankalinsa game da rahoton al'umma. A Landan ne ya lura cewa baya ga jaridun ƙasa da na birni akwai jaridu da ke yi wa al’umma hidima musamman ya yanke shawarar idan ya dawo gida Najeriya zai kafa jaridar al’umma a sashin Ikorodu.

Ya kammala makarantar aikin jarida a Landan a shekara ta 1977, kuma bai taɓa shiga wata sana'a ba in ban da aikin jarida.[3]

Sana'a[gyara sashe | gyara masomin]

Lokacin da ya isa Najeriya, Monsur Olowosago ya yi aiki a jaridar National Concord. An kafa jaridar Concord a 1980, kuma ya nemi aiki a can; An ɗauke shi aiki a ƙarƙashin Marigayi Dele Giwa a matsayin Karamin Edita. Ya yi aiki da Jaridar Concord na tsawon shekaru biyar kafin ya yanke shawarar kafa jaridar al’umma ta Oriwu Sun Community Newspaper. Ya fara samar da jarida ne a shekarar 1985, wato ranar haihuwarsa. Ya fara jaridar ne da ma’aikatansa su biyu da kuma ‘yan jarida uku. An yi aikin ne daga gidan mahaifinsa da ke Ikorodu. Ya fara samar da Jarida mai shafuka 20 baki da fari. A yau suna samar da shafuka sama da 100, da fefa masu launuka.[3][4]

Aiki wa al'umma[gyara sashe | gyara masomin]

Alhaji Monzor Olowosago yana ba da gudummawa ga al'ummarsa a Ikorodu. Shi ne majibincin ƴan jarida da kwararrun ƴan jarida na al’ummar jihar Legas kuma ya ba da kyautar katafaren gini mai ajujuwa 3 ga makarantar firamare ta Estate da ke Ikorodu. Ya kuma gina wani Masallaci a cikin harabar sabuwar cibiyar lafiya ta NASFAT da aka gina a Ikorodu.[5][6]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 "Buhari greets Olowosago, publisher of foremost community newspaper, at 70 | Encomium Magazine" (in Turanci). May 14, 2021. Retrieved 2022-09-12.
  2. "Buhari belatedly rejoices with Olowosago, publisher of Oriwu Sun" (in Turanci). Retrieved 2022-09-12.
  3. 3.0 3.1 "'There is need for more community newspapers in Nigeria'". The Guardian Nigeria News – Nigeria and World News (in Turanci). January 22, 2019. Retrieved 2022-09-12.
  4. oriwusun (June 30, 2020). "MONZOR OLOWOSAGO: I've carved my name in the history of community journalism in Nigeria". Oriwusun Newspapers (in Turanci). Retrieved 2022-09-12.
  5. "NASFAT Ikorodu Commissions Health Centre, Ratibi Mosque –" (in Turanci). July 25, 2022. Retrieved 2022-09-12.
  6. "Publisher donates building to Lagos primary school The Nation Newspaper". The Nation Newspaper (in Turanci). December 24, 2017. Retrieved 2022-09-12.