Muhuyi Magaji Rimin Gado

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Muhuyi Magaji Rimin Gado
Rayuwa
Sana'a

Muhuyi Magaji wani ɗan siyasa ne kuma ɗan gwagwarmaya mai rajin yaƙi da cin hanci da rashawa a jihar Kano da kare hakkin dan Adam.

Bayyanar Muhuyi Magaji[gyara sashe | gyara masomin]

Al’ummar jihar Kano sun fara sanin sunan Muhuyi Magaji Rimin Gado, a cikin shekarar 2010 lokacin da ya gurfanar da gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Ibrahim Shekarau a gaban kuliya, bisa nuna ƙin amincewarsa da naɗin ƴan siyasa a matsayin kantomomin riƙo, wanda hakan ya saɓa da kuma doka.

Muhuyi Magaji ya shigar da ƙarar ne yana neman kotu ta yi fassara kan sashi na Hamsin da Takwas karamin sashi na daya wanda ya baiwa gwamna da majalisa damar nada shugabannin kananan hukumomi, wanda a cewar mai karar, ta ci karo da sashi na Bakwai karamin sashi na daya a kundin tsarin mulkin Nigeria na shekarar 1999.

Muhuyi Magaji Rimin Gado
Muhuyi Magaji Rimin Gado

Muhuyi Magaji ya yi nasara akan gwamnatin jihar Kano, inda mai shari’a Muhammad Sadi Mato ya umarci gwamnan jihar Kano da kwamishinan shari’a da su nada mutanen da za su riki ragamar kananan hukumomin jihar Kano 44 har zuwa lokacin da hukumar zaben jihar za ta iya gudanar da zabe nan da dan lokaci.Ya taɓa dakatar da rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi na riƙo a jihar Kano bayan da ya kai ƙorafi kotu, lokacin dai da yake matsayin mataimakin shugaban ƙaramar hukumar.

Bayan da Gwamna Rabi'u Musa Kwankwaso ya koma mulki a shekarar 2015, Muhuyi ya zama jami'in ƙaramar hukuma na farko da ya mayar da motar gwamnati, wanda hakan ya tilasta wa sauran shugabannin ƙananan hukumomi mayar da nasu.

Ya ce ya yi hakan ne don tsayawa a kan gaskiya. Sai dai hakan ya jawo masa matuƙar baƙin jini a wajen takwarorinsa a lokacin.

Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

A lokacin gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau tsakanin 2003 zuwa shekarar 2011 yayin da Muhuyi yake matsayin mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Rimin Gado, ya taɓa kai ƙorafi ga hukumar EFCC ta ƙasa kan wasu kuɗaɗen ƙaramar hukumar da suka maƙale.

A lokacin da kuɗin suka fito yana riƙon shugabacin ƙaramar hukumar, kasancewar shugaban ƙaramar hukumar ya yi tafiya. Kuma nan take ne ya fara gudanar da wasu ayyukan cigaba da kuɗaɗen a ƙaramar hukumar, lamarin da ya ja babu shiri shugaban ƙaramar hukumar ya dawo daga wata tafiyar da ya yi.

Wannan abu ya jawo saɓani tsakaninsa da shugaban ƙaramar hukumar ta Rimin Gado. Lamarin nan ya fara fito da Muhuyi a idon al'umma a matsayin mai yaƙi da cin hanci da rashawa.

Gwagwarmaya[gyara sashe | gyara masomin]

Ya kafa wata ƙungiya mai zaman kanta wacce ke yaƙi da cin hanci da rashawa, kuma bayan nan ne Gwamna Abdullahi Umar ganduje ya naɗa shi shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano a shekarar 2016.


Shugabancin hukumar yaki da cin hanci da rashawa da karbar koke-koken al'umma

Bayan Abdullahi Umar Ganduje ya zama gwamnan jihar Kano a shekarar 2015, ya naɗa Muhuyi Magaji Rimin Gado a matsayin shugaban hukumar karbar korafi da yaƙi da karɓar rashawa ta jihar Kano. Wannan muƙami da ya samu ya sanya masu sharhi akan al’amuran yau da kullum su ke kallon an ajiye ƙwarya a gurbinta la’akari da yadda aka naɗa jarumi kuma marar tsoro, matashi mai zuciyar ƴaki da rashawa da cin hanci da ƙoƙarin ganin an kakkaɓe dukkanin wata rashawa.

A lokacin da yake shugabantar hukumar ya koma ya yi karatun shari'a inda ya zama lauya.

Lokuta da dama ya sha nanata cewa Ba za mu ragawa duk wanda mu ka samu da karɓa ko bayar da cin hanci ba Archived 2021-07-13 at the Wayback Machine

Wasu masu sharhi kan al'amuran yau da kullum sun ce Muhuyi ya matukar ɗaga darajar hukumar ta cin hanci da rashawa ta jihar Kano, har ta zama hukumar da jami'an gwamnati da attajirai da 'yan kasuwa da sarakai suke tsoronta.

A lokacin da yake riƙe da wannan muƙami ya janyo ce-ce-ku-ce sosai inda ya dinga rigima da ɓangarori daban-daban.

Ya yi rigima da ma'ikatan kotu, ya binciki alƙalai, ya binciki manya-manyan ƴan siyasa, ya binciki Masarautar Kano Archived 2021-07-13 at the Wayback Machine har sau biyu duk kan zargin almundahana da ɓarnata kudaɗen gwamnati.

Sai dai wasu na yi masa zargin cewa ana amfani da shi don cimma wasu burikan siyasa, zargin da ya sha musantawa inda yake cewa yana aikinsa tsakaninsa da Allah.

Tsaka Mai Wuya[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Rawar Da Ya Taka A Rikicin Masarautar Kano Da Gwamnatin Jihar Kano (I) A lokacin rikicin masarautar Kano (zamanin Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II) da gwamnatin jihar Kano akan zargin badaƙalar cin hanci da rashawa da ya dabaibaye masarautar Kano, a nan ma sunan Muhuyi Magaji ya ƙara fitowa domin sai dai shafukan sada zumunta na zamani su ka cika su ka batse da sunan wannan ɗan taliki, la’akari da irin rawar da ya taka akan wannan rikici. Muhuyi Magaji ya karci ƙasa tare da shan alwashin zai aikinsa akan wannan batu babu siyasa ko son ran gwamnati, inda ya fara da gayyatar wasu daga cikin manyan hakiman fadar Kano, da matan marigayi Sarkin Kano Ado Bayero, a ƙarshe ma mai gaba ɗaya ya yi inda ya buƙaci Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II da ya bayyana a gaban hukumar karɓar ƙorafi da yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, domin ya kare kan sa akan zargin cin hanci da ake masa.
  2. Rawar Da Ya Taka A Rikicin Masarautar Kano Da Gwamnatin Jihar Kano (II) Batun Gayyatar Iyalan Marigayi Dr. Ado Bayero Archived 2021-07-13 at the Wayback Machine
  3. Rawar Da Ya Taka A Rikicin Masarautar Kano Da Gwamnatin Jihar Kano (III) Hukumar Yaƙi Da Rashawa Ta Kama Wasu Ma’aikatan Masarautar Kano Archived 2021-07-13 at the Wayback Machine
  4. Muhuyi Magaji Da Ƴan Kasuwar Jihar Kano Bayan da aka samu ɓullar annobar cutar nan ta Korona birus a jihar Kano, gwamnatin jihar Kano ta yanke shawarar sanya dokar hana zirga-zirga da nufin hana yaɗuwar wannan cuta. Mutane sun bi wannan doka sau da ƙafa, ta hanyar zamansu a gida. Amma katsam sai ƴan kasuwar jihar Kano su ka tashi farashin kayan masarufi, al’ummar jihar Kano sun nuna takaicinsu game da yadda suka samu farashin kayayyaki a kasuwannin, inda ya yi tashin gwauron zabi, yayin da suka dora alhakin hakan akan ƴan kasuwa Jin halin da al’umma su ka tsinci kan su a halin ƴan kasuwar jihar Kano, ya sanya hukumar karɓar ƙorafin jama’a da yaƙi da cin hanci da rashawa, ƙarƙashin jagorancin Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya kafa kwamitin yaƙi da masu ɓoye kayan masarufi da nufin cin ƙazamar riba.
    Biyo bayan fara ƙwace kayan da ‘yan kasuwar suka ɓoye da nufin cin ƙazamar riba da Hukumar Karɓar Ƙorafe-Ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano ta yi, ƴan kasuwar Kano sun amince su rage farashin buhun sukari daga N28,000 zuwa N16,000. Hakazalika, hukumar karɓar korafi da yaƙi da karɓar rashawa ta jihar Kano, ta sake waiwayar masu sayar da shinkafa inda aka cimma matsaya akan yarjejeniyar sayar da buhun shinkafa akan naira 16,000. A cikin irin jajircewar Muhuyi Magaji Rimin Gado ya kai ziyarar bazata zuwa katafareren shagon nan na Jifatu da ke kan hanyar Zaria, a cikin birnin Kano, inda ya tarar da suna daga cikin wadanda su ka yi kunnen ƙashi da yarjejeniyar da aka cimma, inda nan ta ke ya sanya aka garƙame wannan katafareren sahgon na Jifatu, tare kuma da yin sammacin babban manajan shagon sayar da kayan masarufi na Sahad da ya bayyana a gaban hukumar.
  5. Muhuyi Magaji Da Ƴan Siyasa Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, ya ƙaddamar da rabon kayan abinci ga masu ƙaramin ƙarfi a jihar Kano, da nufin ragewa al’umma halin raɗaɗin da su ka tsinci kan su. Amma abin takaici da Allah wadai sai gashi an samu wani shugaban ƙaramar hukuma a jihar Kano ya yi abin da bai dace ba, ya canza tsarin da gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi na taimakawa masu ƙaramin ƙarfi, inda ake zargin ya rabawa jami’an ƴan sanda, jami’an shige da fice, da kuma jami’an ƴan sandan farin kaya da kuma ƴan hisba tallafin da aka ce a baiwa masu ƙaramin ƙarfi. Jin wannan labari ya sanya hukumar da Muhuyi ke jagoranta ya yi sammaci tare da tsare shugaban wannan ƙaramar hukuma ta Kumbutso, wato Sagir Abdulkadir Panshekara. An Kama Shugaban Ƙaramar Hukumar A Kano Saboda Karkatar Da Kayan Tallafi Archived 2021-07-13 at the Wayback Machine
  6. Mataimakin gwamnan Kano Nasiru Gawuna ya faɗa komar zargi Archived 2021-07-13 at the Wayback Machine

Dakatarwa daga shugabancin hukumar PCAC[gyara sashe | gyara masomin]

Aranar 5 ga watan Yuli na 2021, majalisar Dokokin Jihar Kano ta dakatar da Barista Muhyi Magaji Rimin Gado saboda kin karbar sabon akantan da Akanta Janar na Jihar Kano ya tura wa hukumar. Amma sai dai wasu majiyoyin sun bayyana babban dalilin dakatar da Muhuyi Magaji Rimin Gadon Archived 2021-07-14 at the Wayback Machine duk kuwa da cewa a nata bangaren majalisar jihar Kano wacce ta sanar da dakatarwar, ta ce, daukar matakin ya biyo bayan kin yin ladabi ga ofishin babban akantan jihar, ta hanyar kin amincewa da wani ma'aikaci da aka turawa hukumar yakin da cin hancin a matsayin babban akanta mai kirga lisaafi, daga bisani ,ma har shi Muhyi Magajin ya rubutawa akantan nadin takardar cewa An ki karbarka kuma ka kama gabanka'

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

BBC Hausa Labarai24 Archived 2021-07-13 at the Wayback Machine