Rabi'u Musa Kwankwaso

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Simpleicons Interface user-outline.svg Rabi'u Musa Kwankwaso
mamba a majalisar dattijai ta Najeriya

9 ga Yuni, 2015 -
District: Kano Central (en) Fassara
gwamnan jihar Kano

Mayu 2011 - Mayu 2015
Ibrahim Shekarau - Abdullahi Umar Ganduje
Ministan Tsaron Najeriya

ga Yuli, 2003 - ga Augusta, 2006
Theophilus Yakubu Danjuma - Thomas Aguiyi-Ironsi
gwamnan jihar Kano

Mayu 1999 - Mayu 2003
Aminu Isa Kontagora - Ibrahim Shekarau
mamba a majalisar wakilai ta Najeriya

1993 -
Rayuwa
Haihuwa Madobi, 21 Oktoba 1956 (66 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Hausa
Karatu
Makaranta Middlesex University (en) Fassara
Loughborough University (en) Fassara
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party
All Progressives Congress
New Nigeria Peoples Party (en) Fassara
kwankwaso.com

Muhammad Rabi'u Musa Kwankwaso (An haifi Rabiu Musa Kwankwaso a ranar Lahadi, 21 ga watan Oktoba na shekarar alif ɗari tara da hamsin da shida (1956), a ƙauyen Kwankwaso da ke a ƙaramar hukumar Madobi ta jahar Kano a Najeriya, Rabiu Musa ya halarci makarantar firamare a garin Kwankwaso, inda daga nan ya samu ci gaba izuwa makarantar kwana ta Gwarzo, duk dai a neman ilimin firamare. Sannan sai makarantar ƙere-ƙere da ke a garin Wudil da kuma kwalejin fasaha ta Kano. Bayan daga nan ya garzaya makarantar kimiyya da fasaha ta Kaduna polytechnic da ke a garin jahar Kaduna. A inda ya samu yin difloma a fannin kimiyya da fasaha ta ƙasa,da babbar diploma duk a fannin kimiyya da fasaha. Ya samu yin makarantar gaba a garin London da ke ƙasar Ingila a kwalejin Middlesex a shekara ta alif ɗari tara da tamanin da biyu zuwa da uku (1982 zuwa 1983), Kwankwaso ya ci gaba da karatunsa a jami’ar fasaha da ke Loughborough a ƙasar Ingila a shekarar alif ɗari tara da tamanin da uku zuwa da biyar (1983 zuwa 1985) inda ya samu lambar babban digiri mai suna Masters a turance a fannin fasahar ruwa. Kwankwaso ya kasance haziƙin mutum ne a kusan dukkan lokutan karatunsa musamman ta ɓangaren tsayawa da ya yi domin ganin cewa ya kammala karatu cikin nasara kuma ba tare da ɓata lokaci ba. Ya kasance ɗalibi wanda kullum ya ke a sawun gaba wajen karatu da yin dukkan wani aikin aji da akan bashi. An zaɓi Kwankwaso a matsayin shugaban ɗalibai a lokacin karatunsa, sannan ya kasance zaɓaɓɓe a ƙungiyar ɗalibai ta jihar Kano. ɗan siyasar Najeriya ne. Ya riƙe matsayin gwamna a jahar Kano har sau biyu, wato a shekara ta (1999 zuwa 2003), da kuma shekara ta (2011 zuwa 2015), Shi ne Gwamnan farko na jihar Kano a jamhuriya ta huɗu kuma ya ci zaɓe ne duk a ƙarƙashin jam'iyyar PDP kafin daga bisani ya chanza jam'iyya ya koma jam'iyyarsa ta APC. A zaɓen shekara ta (2003), Alh. Rabiu Musa Kwankwaso ya yi rashin nasara ne a hannun Mal.Ibrahim Shekarau. A watan Yuli a shekara ta (2003), Olusegun Obasanjo ya naɗa shi a matsayin Ministan tsaron Najeriya bayan samun rashin nasara da ya yi a zaɓen.

A shekara ta( 2015), Kwankwaso ya yi rashin nasara a hannun Shugaba Muhammadu Buhari a zaben fidda gwani na dan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar APC, daga bisani sai ya chanza sheka zuwa takarar kujerar Sanata Wanda a nan ne ya samu nasarar cin zaben. A shekara ta( 2018), ya fice daga jam'iyyarsa ta( APC) inda ya sake komawa jam'iyyarsa ta da wato (PDP) da niyyar yin takarar Shugaban ƙasa, sai dai bai samu nasara a zaɓen fidda gwani ba wanda aka gudanar a garin Fatakwal.Ana masa lakabi da "kwankwansiyyah". Mukamai

Kwankwaso ya riƙe muƙamai da yawa a Jahar Kano dama ƙasar Najeriya baki ɗaya, wadanda suka haɗa da aikin gwamnati dana siyasa baki ɗaya.

A shekara ta( 2003), bayan ya faɗi zaɓe a karo na biyu a takatar Gwamnan Jihar Kano Shugaban Kasa Olusugun Obasanjo ya naɗa shi a matsayin babban Ministan Tsaron Najeriya wanda ya riƙe na tsawon shekaru huɗu. Sannan an sake naɗa shi a matsayin Jakadan Najeriya a Dafur dake Ƙasar Sudan a ƙarƙashin gwamnatin Umar Musa Yar’adua .

1. Mataimakin Kakakin Majalisar Tarayya a watan Janairu a shekara ta ( 1992) zuwa watan Nuwamba a shekara ta( 1993)

2 Gwamnan Jihar Kano 29 ga watan Mayu a shekara ta( 1999) zuwa( 29 ) ga watan Mayu a shekara ta (2003) 3. Ministan Tsaro na Kasa watan – Yula shekara ta ( 2003 ) zuwa shekara ta ( 2007) 4. Babban Jakadan Najeriya a Dafur A shekara ta ( 2007) zuwa shekara ta (2011) 5. Gwamnan Jahar Kano – (29 ) ga watan Mayu a shekara ta (2011) zuwa( 29 ) ga watan Mayu a shekara ta ( 2015) 6. Satanan Kano ta Tsakiya –( 11 ) ga watan Yuni a shekara ta ( 2015 ) zuwa shekara ta ( 2019).

An zabi Muhammad Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin Sanata daga Kano ta tsakiya a zaben dubu biyu da sha biyar (2015) wanda ya tsaya bayan faduwarsa zaben share fagen tsayawa takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC.

Tarihin sa[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso a ranar( 21), ga watan Oktoban shekara ta( 1956), a ƙauyen Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi ta jahar Kano.[1] Ya halarci makarantar firamaren gwamnati ta garin Kwankwaso, sai Makarantar sakandiren kwana ta Gwarzo sai yaje makarantar kere-kere ta garin Wudil Makarantar fasaha a Kano kafin daga bisani ya halarci makarantar Kaduna Polytechnic a inda ya samu shaidun difiloma guda biyu (karamar difiloma da babbar difiloma) wato National Diploma da Higher National Diploma ya yi kuma digirinsa na farko a Birtaniya Middlesex Polytechnic (1982-1983),da kuma Loughbrough University of Technology a shekara ta (1983zuwa1985)inda ya yi babban digirinsa wato Masters Degree.[2] Dukkan yawancin makarantun da Kwankwaso yayi karatu shi ne yake rike mukamin shugaban daliban makarantun kuma an taba zaɓarsa a matsayin shugaba.

Fara tashensa[gyara sashe | gyara masomin]

Rabiu musa kwankwaso da kuma rochas okoracha

Kwankwaso ya fara aiki a shekarar ta( 1975) inda ya fara aiki da hukumar ruwa ta jahar Kano, wato Kano State Water Resources and Engineering Construction Agency wato WRECA ya yi aiki na tsawon shekaru( 17), a bangarori daban-daban inda har ya zama shugaban ma'aikatar. A shekarar ta ( 1992), aka zaɓi Kwankwaso ɗan majalisar wakilai ta taraiyar Najeriya mai wakiltar ƙaramar hukumar Madobi. Kuma shi ne ya zama mataimakin kakakin majalisar a ƙarƙashin jamiyyar PDP A wani taro da akayi na gyaran kundin mulkin kasa, an zabi kwankwaso a matsayin wakilin jihar Kano. Ya shiga jam'iyyar PDP a shekara ta (1998).

Zamansa Gwamna[gyara sashe | gyara masomin]

An zabi Rabiu Kwankwaso a matsayin gwamnan jahar Kano a shekara ta( 1999), karkashin jam'iyyar( PDP), har zuwa shekara ta( 2003), inda ya yi rashin nasara a hannun Ibrahim Shekarau. Kasantuwar sa gwamna a jahar Kano, ya zama wani babban al'amari da ya faru a jahar kano, kamar yadda Kwankwaso ya ke nuna cikakken goyon baya ga tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo. Tare da yadda ya kirkiro wasu tsarurruka na musamman a gwamnatinsa da kuma yadda rashin nasarar sa ta kasance a hanun tsohon gwamna Ibrahim Shekarau.Sai dai kuma Kwankwaso ya sake nuna sha'awar tsayawa takara a zaben shekara ta( 2007), amma hakan bata yiyuba sakamakon samunshi da wasu laifuffuka da gwamnatin Ibrahim Shekarau ta jam'iyyar ANPP ta yi. Sai kwankwaso ya kawo wanda zai yi takarar a jam'iyyar PDP wato Ahmad Garba Bichi.

Taron Kwankwasiyya kenan, a jihar kano
yan kwankwasiyya a jihar kano
Yadda kwankwaso ya maida kofar nasarawa kenan ta zamani

Kwankwaso bai yi ƙasa a gwiwa ba wajen sake tsayawa takar gwamna a zaben shekara ta ( 2011 ), kuma ya yi nasarar kayar da jam'iyyar ANPP ta Salihu Sagir Takai. An yi zaben ranar (26) ga watan Afrilun shekara ta (2011), kuma ya kama rantsuwar aiki a ranar (29), ga watan Mayu shekara ta( 2011), Kwankwaso na daga cikin Gwamnoni guda biyar wato( G-7 ) waɗanda suka fita daga jam'iyyar su ta PDP tare da sauya sheka zuwa APC.

Akidar siyasar Rabiu Musa Kwankwaso Duba Kwankwasiyya

.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. https://www.africa-confidential.com/profile/id/3939/Rabiu_Kwankwaso
  2. https://blerf.org/index.php/biography/kwankwaso-rabiu-musa/