Ishaya Shekari

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ishaya Shekari
gwamnan jihar Kano

1 Satumba 1978 - Oktoba 1979
Sani Bello - Abubakar Rimi
Rayuwa
Haihuwa Zangon Kataf, 3 ga Augusta, 1940 (83 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Yaren Tyap
Karatu
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Yaren Tyap
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Ishaya Shekari. Soja, mai muƙamin 'Air Vice Marshal', ya zama gwamnan Jihar Kano na uku a cikin shekarar 1978.

Farkon rayuwa da Karatu[gyara sashe | gyara masomin]

An haife shi a ranar 3 ga watan Agusta na shekarar 1940 (3 August, 1940) a garin Zangon-Kataf da ke cikin ƙaramar hukumar Kaciya ta Jahar Kaduna . Wanda yanzu ta zama ƙaramar hukumar Zangon-Kataf ta jahar Kaduna. [1]

Ya fara karatu a ƙaramar fimare da ke Zango-Kataf a shekarar 1950 zuwa 1953. Daga nan kuma ya shige makarantar tsakiya (Middle School) da ke Zariya , a shekarar 1954, inda daga baya ya samu wucewa babbar firamare da ke Soba (Senior Primary School Soba) da ke Zariya, a shekarar 1956. Ya shiga secondary (Provincial Secondary School) da ke Zariya, daga 1957 zuwa 1962. Sannan kuma ya samu zuwa Birtaniya a cikin shekarar 1969, inda ya halarci wani horo na musamman na tsawon watanni uku a makarantar ‘Royal Air Force Junior Command and Staff School Term Hill'.

Haka nan a cikin shekarar 1970, ya sake komawa Birtaniya inda ya samo horo a kan ‘Combatant Air Force Officer’. Wannan horo ya ɗauke shi har tsawon shekara guda wanda ya yi shi a makarantar ‘Royal Air Force College’ da ke Bracknell ta ƙasar Birtaniya'.

Aikin Soja[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan kammala karatunsa na sikandire, ya samu nasarar shiga makarantar soja mai suna ( Nigerian Military Training College) a watan Nuwamba na shekarar 1962. A shekarar 1963, ya tafi zuwa ƙasar Kanada dan halartar horon tuƙin jirgin sama a makarantar ‘Royal Canadian Air Force’ daga watan Yuli na shekarar 1964 (June 1964) zuwa watan Juli na shekarar 1966 (June 1966). [2]

Ayyuka da Muƙamai[gyara sashe | gyara masomin]

Air Vice Marshal' Ishaya Aboi Shekari, ya bayar da gagarumar gudunmawa a wannan fanni nasa na sojan sama kafin ya zama gwamnan Kano. da farkon farawa ya fara da zama ofisa tare da rundunar sojojin saman Nijeriya inda ya yi aiki a Reshen Horas da Sojojin Saman Nijeriya (Nigerian Air Force Training Wing) na tsawon watanni tara kafin a tura shi zuwa helikwatar sojojin saman Nijeriya (Nigerian Air Force Headquarters) da ke Legas a matsayin jami’i (Operations Officer). Ya riƙe wannan muƙami tun daga 1967 har zuwa 1968. An sake tura shi Kaduna a matsayin jami’i mai bada horo a kan jan akalar jirgi (Instructor on Navigation).

A cikin shekarar 1969, an ɗaukaka muƙaminsa zuwa jami’i ma bada umarni a sashen sojojin sama na makarantar tsaron Nijeria (Officer Commanding Air Force Wing of Nigerian Defence Academy). Ya riƙe muƙamin babban jami’in sojan sama na helikwatar rudunar sojojin saman Nijeria (Senior Air Force Officer Logistics), daga 1971 zuwa 1974, kafin a canja shi zuwa babban jami’in sojan sama mai kula da harkokin mulki (Senior Staff Officer with Administratiɓe Branch of Nigerian Air Force). Sannan kuma dai aka sake ɗauke shi daga wannan sashe na mulki zuwa sashen aiwatarwa nan ma a matsayin babban jami’i (Senior Staff Officer with Operations Branch). Duka wannan a babbar helikwatar sojan saman Nijeriya ne da ke Legas.

A shekarar 1975, aka yi masa muƙamin kwamanda a rundunar sojan saman Nijeriya ɓangaren Lojistik (Commander Nigerian Air Force Logistics Group, Ikeja). Sannan kuma aka sake mayar da shi helikwata a matsayin jami’i ma kula da lojistiks na rundunar sojan saman Nijeriya (Air Force Officer in-Charge of Logistics). [3]

Gwamnan Kano[gyara sashe | gyara masomin]

A shekarar 1978 aka yi masa tagwan muƙamai a Kano. A lokacin da yake riƙe da ragamar shugabancin Kano (gwamna), sannan kuma yake riƙe da kujerar kwamanda 303 F.T.C ta Kano. Ya riƙe waɗannan muƙamai guda biyu tun daga 1978 zuwa 1979 inda aka yi zaɓen jamhuriya ta biyu sannan ya miƙa mulki a hannun gwamnan farar hula Marigayi Alhaji Muhammad Abubakar Rimi . Barinsa Aikin Soja Muƙaminsa na ƙarshe shi ne zamowarsa ministan ayyuka na musamman a gwamnatin Janar Ibrahim Badamasi Babangida , wanda daga nan ya bar aiki.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2021-12-01. Retrieved 2021-11-27.
  2. "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2021-11-27. Retrieved 2021-11-27.
  3. https://military-history.fandom.com/wiki/Ishaya_Shekari