Salihu Sagir Takai

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Salihu Sagir Takai
Rayuwa
Haihuwa Takai, 20 Disamba 1955 (68 shekaru)
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

Salihu Sagir Takai dan siyasan Najeriya ne, masanin ilmi, ya kasance Kwamishina na Gwamna Malam Ibrahim Shekarau kuma tsohon Shugaban Karamar Hukumar Takai da ke a Jihar Kano, ya yi takaran Gwamna sau 3 a jam’iyyu daban-daban guda uku ANNPP wadda daga baya ta hade da sauran jam'iyyun suka kafa, APC a shekara ta (2011). PDP a shekara ta (2015). Da kuma PRP a shekara ta (2019). Inda daga baya kuma ya sake komawa jam'iyyar APC a sheksrsr 2020 bayan ya fadi zabe a shekarar 2019.[1]

Rayuwar farko[gyara sashe | gyara masomin]

Salihu haifaffen karamar hukumar Takai ne da ke jihar Kano, ya halarci makarantar firamare ta Kwalli, a cikin garin Kano .[Ana bukatan hujja]

Harkar siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

An zabi Salihu a matsayin Shugaban Karamar Hukumar Takai yayin da Injiniya Rabiu Kwankwaso ya kasance Gwamnan Jahar Kano tsakanin Shekara ta 1999 zuwa shekara ta 2002, Salihu Ya zama Kwamishina bayan an zabi Malam Ibrahim Shekarau a matsayin Gwamnan Jihar Kano a shekara ta 2003 Babban zaben Najeriya. Shekarau ya shafe Takai a matsayin rusasshiyar jam’iyyar All Nigeria Peoples Party ANPP a yanzu All Progressive Congress APC, dan takarar Gubernatorial a shekara ta 2011 a babban zaben Najeriya wanda Rabiu kwankwaso na Peoples Democratic Party (PDP) Salihu ya kayar kuma shi ne Nominee na Peoples Democratic Party (PDP) a babban zaben shekara ta 2015 inda Dr Abdullahi Umar Ganduje na All Progressive Congress (APC) ya kayar da shi har ma ya taya Gwamnan murna kafin a sanar da sakamakon zaben a hukumance. A shekarar 2018 Takai ya koma PRP bayan da Rabiu Kwankwaso yana da Abba Kabir Yusuf a matsayin dan takarar gwamna karkashin jam’iyyar Peoples Democratic Party Takai ya zama tutar jam’iyyar PRP inda ya zabi Kabiru Muhammad Gwangwazo a matsayin nasa abokin takara a babban zaben 2019 na Najeriya bayan sake zaben Gwamna Abdullahi Umar Ganduje a karo na biyu, Takai ya koma jam'iyyar APC kuma ya bi tsohon maigidansa Malam Ibrahim Shekarau

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Hamisu, Ibrahim (28 July 2020). "Salihu Sagir Takai Ya Sake Komawa Jam'iyyar APC". Ts=askar Labarai. Archived from the original on 5 March 2023. Retrieved 5 March 2023.