Navi Pillay

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Navi Pillay
ICDP commissioner and Vice president (en) Fassara

ga Afirilu, 2015 -
United Nations High Commissioner for Human Rights (en) Fassara

1 Satumba 2008 - 31 ga Augusta, 2014
Judge of the International Criminal Court (en) Fassara

11 ga Maris, 2003 - 31 ga Augusta, 2008
Rayuwa
Haihuwa Durban, 23 Satumba 1941 (82 shekaru)
ƙasa Afirka ta kudu
Karatu
Makaranta University of Natal (en) Fassara
Harvard Law School (en) Fassara
Matakin karatu doctorate (en) Fassara
Harsuna Turanci
Sana'a
Sana'a mai shari'a da Lauya
Employers Majalisar Ɗinkin Duniya
Kyaututtuka
Mamba Permanent United Nations Fact Finding Mission on the Israel Palestine conflict (en) Fassara
Navi Pillay

Navanethem "Navi" Pillay (an haife ta ranar 23 ga watan Satumba shekara ta 1941) ƙwararriyar masaniyaf shari'a ce ta Afirka ta Kudu wanda ta yi aiki a matsayin Babbar Kwamishinan Kare Haƙƙin Dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya daga 2008 zuwa 2014.'Yar Afirka ta Kudu 'yar asalin Tamil ta Indiya, ita ce mace ta farko da ba farar fata ba a Kotun Koli ta Afirka ta Kudu,[1] kuma ta yi aiki a matsayin alkaliya ta Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya da Shugabar Kotun Hukunta Laifukan Ruwanda. .Wa'adinta na shekaru huɗu a matsayin Babban Kwamishinan a hukumar kare Ƴancin Ɗan Adam ya fara a ranar 1 ga Satumba 2008[2] kuma an ƙara ƙarin shekaru biyu a 2012.[3] Yarima Zeid bin Ra'ad ne ya gaje ta a watan Satumban 2014.A cikin Afrilun shekarar 2015 Pillay ta zama Kwamishina ta 16 na Hukumar Yaƙi da Hukuncin Kisa ta Duniya. Har ila yau, tana ɗaya daga cikin manyan mutane 25 a hukumar yaɗa labarai da dimokuraɗiyya da ƙungiyar masu rajin kare hakkin bil'adama ta Reporters Without Borders ta kaddamar.[4]

Fage[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Pillay a shekara ta 1941 a wata matalauta unguwar Durban, lardin Natal, Tarayyar Afirka ta Kudu.[1] Ita 'yar asalin Tamil ta Indiya ce kuma mahaifinta direban bas ne.[1] Ta auri Gaby Pillay, lauya, a cikin Janairu 1965.[5] Tana da 'ya'ya mata biyu.

Navi Pillay

Al'ummar Indiya sun tallafa mata da gudummawa,[6][7] ta kammala karatu daga Jami'ar Natal tare da BA a shekarar 1963 da LLB a 1965. Daga baya ta halarci Makarantar Shari'a ta Harvard, ta sami LLM a 1982 da kuma Dikita na Digiri na Kimiyyar Shari'a a 1988. Pillay ita ce 'yar Afirka ta Kudu ta farko da ta sami digiri na uku a fannin shari'a daga Makarantar Shari'a ta Harvard.[8]

Kyaututtuka[gyara sashe | gyara masomin]

A cikin shekarar 2003, Pillay ta sami lambar yabo ta Gruber don 'Yancin Mata.

An ba ta digirin girmamawa

  • Jami'ar Fasaha ta Durban - Jami'ar da ke garinsu na Durban, Afirka ta Kudu,
  • Jami'ar Durham,
  • Makarantar Shari'a ta Jami'ar City ta New York,
  • Makarantar Tattalin Arziki ta London, Jami'ar Rhodes,
  • Jami'ar Leuven

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. 1.0 1.1 1.2 Reuters (28 July 2008). "FACTBOX-South Africa's Pillay is new human rights chief". Retrieved on 30 July 2008.
  2. Office of the United Nations High Commissioner for Human Rights (2008). "Navanethem Pillay confirmed as new High Commissioner for Human Rights". Retrieved on 30 July 2008.
  3. Navanethem Pillay
  4. International Criminal Tribunal for Rwanda (1999). Fourth annual report to the United Nations Archived 3 ga Janairu, 2014 at the Wayback Machine. Retrieved on 30 July 2008.
  5. Interview with Vino Reddy (11 August 2002). Voices of Resistance. Retrieved on 30 July 2008.
  6. Jonah Fisher (28 July 2008). "Profile: New UN human rights chief". BBC News. Retrieved on 30 July 2008.
  7. Maggie Farley (26 July 2008). "Human rights commissioner fought a long battle for her own rights". The Sydney Morning Herald. Retrieved on 30 July 2008.
  8. Emily Newburger (Spring 2006). "The bus driver's daughter". Harvard Law Bulletin. Retrieved on 30 July 2008.