Olukayode Ariwoola

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Olukayode Ariwoola
Chief Justice of Nigeria (en) Fassara

27 ga Yuni, 2022 -
Tanko Muhammad
Rayuwa
Haihuwa 22 ga Augusta, 1958 (65 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Yarbanci
Karatu
Makaranta Jami'ar Obafemi Awolowo
Matakin karatu Bachelor of Laws (en) Fassara
Harsuna Turanci
Yarbanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a Lauya

Olukayode Ariwoola (an haife shi a ranar 22 ga watan Agusta shekara ta 1954) masanin shari'a ne ɗan Najeriya kuma mai shari'a na Kotun Ƙoli ta Najeriya wanda ke riƙe da muƙamin babban alƙalin alƙalai na Tarayyar Najeriya. A da ya kasance Alƙalin Kotun ɗaukaka ƙara ta Najeriya, sai kuma a ranar 22 ga watan Nuwamba, shekarar 2011, aka naɗa shi a benci na kotun ƙolin Najeriya a matsayin mai shari’a, wanda babban jojin Najeriya ya rantsar da shi.[1][2] An naɗa shi yana jiran amincewar Majalisar Dokoki ta ƙasa a matsayin babban Alƙalin Alƙalan Najeriya a ranar 27 ga watan Yunin 2022 bayan murabus din Alƙalin Alƙalan Najeriya Tanko Muhammad.[3][4][5][6][7][8]

Rayuwa da kuma karatu[gyara sashe | gyara masomin]

Olukayode Ariwoola

An haifi Ariwoola a garin Iseyin na jihar Oyo, ya fara karatun firamare ne a makarantar Local Authority Demonstration School da ke Oluwole a karamar hukumar Iseyin ta jihar Oyo. Daga nan ya wuce Makarantar Zamani ta Musulmai a wannan Garin daga shekarar 1968 zuwa shekarar 1969. Sannan ya halarci makarantar Ansar-Ud-Deen da ke Shaki ta Jihar Oyo inda ya kammala Sakandare. Ariwoola ya kammala karatunsa na jami'a, a Jami’ar Ife (Jami’ar Obafemi Awolowo a yanzu), a Ile Ife, Jihar Osun inda ya samu digirinsa na farko a fannin shari’a (LLB).

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "10 things you probably don't know about Olukayode Ariwoola, the new acting CJN | Intel Region" (in Turanci). 2022-06-27. Retrieved 2022-06-28.
  2. "Nigeria: CJN Swears in Justice Olukayode Ariwoola As JSC". allAfrica.com. Retrieved 1 April 2015.
  3. "Ariwoola Emerges Acting CJN After Muhammad is Forced Out – THISDAYLIVE". www.thisdaylive.com. Retrieved 2022-06-28.
  4. "Buhari swear in Justice Olukayode Ariwoola as acting CJN". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News (in Turanci). 2022-06-27. Archived from the original on 2022-06-27. Retrieved 2022-06-28.
  5. "BREAKING: Justice Tanko Muhammad resigns As CJN". Punch Newspapers. 2022-06-27. Retrieved 2022-06-27.
  6. Oamen, Samuel (2022-06-27). "BREAKING: CJN Tanko Mohammad resigns The Nation Newspaper". The Nation Newspaper. Retrieved 2022-06-27.
  7. "UPDATED: Buhari to swear in new CJN after Tanko Muhammad's resignation - Premium Times Nigeria" (in Turanci). 2022-06-27. Retrieved 2022-06-27.
  8. "UPDATED: Justice Olukayode Ariwoola Takes Oath Of Office As Acting CJN". Channels Television. Retrieved 2022-06-27.