Rufa'i Garba

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Rufa'i Garba
gwamnan jihar Sokoto

ga Augusta, 1998 - Mayu 1999
Rasheed Adisa Raji - Attahiru Dalhatu Bafarawa
Gwamnan jahar Anambra

21 ga Augusta, 1996 - 6 ga Augusta, 1998
Mike Attah - Emmanuel Ukaegbu
Rayuwa
Cikakken suna Rufai Garba
Haihuwa 29 Mayu 1988 (35 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Hausawa
Harshen uwa Hausa
Karatu
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa

A ranar 20 ga watan Afrilun shekara ta 1996, gwamnatin soja ta hambarar da Alhaji Ibrahim Dasuki, Sarkin Musulmi na 18 a Sokoto. A matsayinsa na Gwamnan Sakkwato a shekarar 1999, Rufai Garba ya amince da sasantawa da Dasuki kuma ya samar masa da tsarin walwala.

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Kyaftin Rukuni (Sojan Sama) Rufa'i Garba ya kasance mai kula da harkokin mulkin soja na Jihar Anambra a kasar Nijeriya daga ranar 21 ga watan Disamban shekara ta alif 1996 zuwa 6 ga watan Agusta shekara ta alif 1998 a lokacin mulkin soja na Janar Sani Abacha, sannan na Jihar Sakkwato daga ranar 6 ga watan Agusta shekara ta alif 1998 zuwa 29 ga watan Mayu shekara ta alif 1999 a lokacin rikon kwarya Gwamnatin Janar Abdulsalami Abubakar, lokacin da ya mika wa zababben Gwamna Attahiru Dalhatu Bafarwa.[1]

Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

A matsayinsa na Gwamnan Anambra ya amince da gina ginin helkwatar hukumar Ilimi ta Jiha, amma ba a yi komai ba har aka fara aiki a shekarar 2009.  A watan Fabrairun shekara ta 1998, gobarar abin da ba a bayyana ba ta kone ofishin gwamnan a gidan Gwamnatin Jihar Anambra.  A watan Agusta shekara ta alif 1998 ya ce 'yan asalin jihar Anambara suna tsoron rundunar yaki da aikata laifuka kamar yadda suke tsoron masu laifi. Ykuma a ce rundunar tana karbar kudi a shingayen hanya tare da tsare mutane ba bisa ka’ida ba, kuma ya ce gwamnati za ta murkushe wannan aiki.[2]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. http://allafrica.com/stories/200912160166.html
  2. http://www.worldstatesmen.org/Nigeria_federal_states.htm