Jump to content

Suraj Adekunbi

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Suraj Adekunbi
Rayuwa
Haihuwa 8 ga Maris, 1975 (49 shekaru)
Karatu
Makaranta Babban Makarantar Sakandare, Aiyetoro
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa All Progressives Congress

Surajudeen Ishola Adekunbi ɗan kasuwar Najeriya ne kuma ɗan majalisar dokokin jihar Ogun, inda shine shugabanta mai ci.[1]

Rayuwar farko[gyara sashe | gyara masomin]

An haife shi a Ayetoro, dake jihar Ogun a kudu maso yammacin Najeriya, Adekunbi yana ɗaya daga cikin ƴaƴa goma sha biyar na Rahmon da Elizabeth Adekunbi.[2]

Ya halarci makarantar firamare ta St. Paul African Church, Ayetoro, kafin ya wuce zuwa makarantar Sakandare ta Aiyetoro, inda ya samu takardar shedar makaranta a shekara ta alif dari tara da casa'in da uku 1993. Ya samu Diploma ta ƙasa a fannin Injiniya daga Federal Polytechnic, Ilaro a shekarar ta alif dari tara da casa'in da shida 1996, sannan ya sami Diploma ta ƙasa a Polytechnic, Ibadan. Daga nan ya sami takardar shaidar kammala karatun digiri a jami'ar fasaha ta tarayya dake Akure, da kuma digiri na biyu a fannin raya ayyuka da aiwatarwa a shekarar 2011 a jami'ar Ibadan.[3]

Sana'a Da Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Adekunbi ya fara aikin sa ne da aiki a matsayin mataimaki na aiki a Kamfanin Bunƙasa Man Fetur (NPDC) da ke Jihar Edo a lokacin da yake hidimar matasa masu yi wa ƙasa hidima a shekarar 2000. Bayan ya yi hidimar Matasa, ya koyarwa a Government Technical College, Idi-Aba, Abeokuta. Daga nan ya shiga ma’aikatan gwamnatin jihar Ogun yana aiki a ofishin sufuri daga shekarar 2004 zuwa 2006, kafin daga bisani ya ajiye aiki ya koma kamfanin mahaifinsa, Al-Rahman Oil & Gas Limited.[3][2]

A shekarar 2007, ya tsaya takarar ɗan majalisar dokokin jihar Ogun a Egbado North (yanzu Yewa North) amma ya sha kaye.[ana buƙatar hujja]A cikin shekarar 2011 ya sake tsayawa jam'iyyar Action Congress of Nigeria (ACN) kuma ya yi nasara. An kuma zaɓe shi a matsayin shugaban majalisa.[4] kuma aka sake zaɓen shi a matsayin Kakakin Majalisa a 2015.[5][6][3]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. http://thenationonlineng.net/adekunbi-returned-as-ogun-speaker/
  2. 2.0 2.1 "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2017-09-06. Retrieved 2023-03-16.
  3. 3.0 3.1 3.2 "Kwafin ajiya". Archived from the original on 2023-03-16. Retrieved 2023-03-16.
  4. https://www.vanguardngr.com/2011/06/ogun-edo-get-new-speakers/
  5. https://thenewsnigeria.com.ng/2015/06/08/adekunbi-returns-as-ogun-assembly-speaker/
  6. https://www.legit.ng/456409-adekunbi-re-elected-ogun-speaker.html[permanent dead link]