Yakin Damasak

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Infotaula d'esdevenimentYakin Damasak
Map
 13°06′18″N 12°30′24″E / 13.105°N 12.5067°E / 13.105; 12.5067
Iri faɗa
rikici
Bangare na Rikicin Boko Haram
Kwanan watan 9 –  17 ga Maris, 2015
Ƙasa Najeriya
Participant (en) Fassara

Yakin Damasak ya faru ne a ranar 18 ga watan Maris shekara ta 2015 lokacin da sojojin Nijar da na Chadi suka kai wa 'yan Boko Haram hari a garin Damasak na Najeriya. An fatattaki ‘yan Boko Haram daga garin bayan kwashe kasa da kwana guda ana gwabza kazamin fada.[1] A ranar 24 ga watan Nuwamban 2014 ne kungiyar Boko Haram suka kwace iko da garin Damasak, kuma ikon na karkashinsu har zuwa karshen wannan yakin. A lokacin da aka kwato garin ya kasance ba kowa.[2] Farar hular da suka rage a cikin garin daga marasa lafiya sai tsofaffin da ba za su iya barin garin ba.[3] Bayan yakin sojojin Chadi sun kafa sansanoni a wajen garin sannan jiragen helikwafta na Chadi guda biyu sun iso da wasu kayayyaki.[4]

Bayan nan[gyara sashe | gyara masomin]

A ranar 20 ga watan Maris, kwanaki biyu bayan yakin, sojojin Nijar da na Chadi sun gano wani wakeken kabari da mutane fiye da 90 aciki a karkashin wata gada dake a wajen birnin.[5][6] Gawarwakin fararen hular sun ji raunika ta hanyar iska ta hamada, wanda ke nuni da cewa an yi kisan kiyashi ne a wani lokaci da ya wuce.[7]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Soldiers drove the terrorists out of Damasak in Borno state [PHOTOS]". Pulse Nigeria (in Turanci). 2015-03-20. Retrieved 2021-01-14.
  2. "Boko Haram was 'driven out' of the northeastern Nigerian town". www.aljazeera.com (in Turanci). Retrieved 2021-01-14.
  3. "'Mass graves' were discovered". France 24 (in Turanci). 2015-03-21. Retrieved 2021-01-14.
  4. "Troops from Chad. Niger freed the Nigerian town from Boko Haram | The Seattle Times". 2015-04-02. Archived from the original on 2015-04-02. Retrieved 2021-01-14.
  5. Aminu Abubakar and Melissa Gray (21 March 2015). "Mass grave found in former Boko Haram-held town". CNN. Retrieved 2021-01-14.
  6. "Mass grave found in recaptured Nigerian town". www.aljazeera.com (in Turanci). Retrieved 2021-01-14.
  7. "Soldiers from Niger and Chad discover at least 70 victims of Boko Haram". Washington Post (in Turanci). ISSN 0190-8286. Retrieved 2021-01-14.