Damasak

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Damasak

Wuri
Map
 13°06′18″N 12°30′24″E / 13.105°N 12.5067°E / 13.105; 12.5067
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
JihaJihar Borno
Ƙaramar hukuma a NijeriyaMobbar
Bayanan Tuntuɓa
Kasancewa a yanki na lokaci

Damasak babban birni ne a ƙaramar hukumar Mobbar, cikin jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya . Tana kusa da yankin kogin Yobe da Komadugu Gana, [1] kusa da kan iyaka da Nijar .

Hanyoyi biyu kanana sun isa Damasak. Daya daga kudu zuwa Gubio da Maiduguri, babban birnin jihar Borno, dayan kuma yayi dodar zuwa Kukawa da Baga .

A cikin 'yan shekarun nan, matsalar kwararowar hamada a arewacin Najeriya ta kasance matsala a garin Damasak. [2]

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

A cewar masana, Kamkama Modu, wani Karde ne daga Bagirmi ya kafa garin . [3]

Damasak wani yanki ne mai ƙarfi ga wayewar Sao a ƙarni na 16, an kuma kewaye shi da shinge ganuwa mai kauri da tsawo. Idris Alooma ne ya ci garin da yaki a cikin shekarar 1570s ko 1580, kamar yadda Ibn Furtu ya rubuta (wanda ke nuna Sao a matsayin "Sao-Gafata"). [4] [5]

Wurin da Damasak yake yanzu ba tabbaci kan cewa a salin wurin ne. [6] Masanin tarihi Graham Connah ya ziyarci yankin a cikin shekarar 1965 tare da wasu gungun mazauna yankin sun ba da rahoton cewa yanzu yankin Damasak tana da kusan kilomita daya 1 daga asalin inda take (inda za'a iya samun motsi), wanda kuma suka bayar da rahoton cewa an watsar dashi a farkon karni na shekarun 1800s amma an kwashe kusan shekaru 100 ana mamaye dasu. [7]

Bajamuse mai bincike Heinrich Barth (1821-1865) ya ba da rahoto a cikin 1850s cewa har yanzu ana iya gano Damasak daga wani kogi da aka sanya wa garin sunan sa, amma a halin yanzu ana kiran wannan kogin da suna "Fatoghana". Ya kuma bayar da rahoton cewa Edris, Sarkin Bornu daga 1353-77, ya mutu a Damasak bisa ga wasu dalilan. [8]

A watan Maris din 2015, an samu gawawwakin mutane 70 a wajen garin. An gano gawarwakin ne bayan ya Boko Haram sun kwace garin . A ranar 24 Maris 2015, mazauna garin sun ce Boko Haram sun kwashe mata da yara sama da 400 daga garin yayin da suke tserewa harin sojoji a farkon wani watan.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. Mortimore, Michael. Adapting to Drought: Farmers, Famines, and Desertification in West Africa, p. 244 (1989)(note 3 notes that the Komadugu Gana joins the Yobe at Damasak)
  2. Murray, Senan (23 January 2007). Nigerian houses swallowed by sand, BBC News
  3. Lange, Dierk. A Sudanic Chronicle: The Borno Expeditions of Idris Alauma (1564-1576) According to the Account of Ahmad b. Furtu, p. 44, 120-21 (1987)
  4. Shillington, Kevin. Encyclopedia of African history, Volume 1, entry on Borno (Bornu), Sultanate of: Mai Idris Alooma (1571-1603), p. 271 (2005)
  5. Diouf, Sylviane. Fighting the Slave Trade: West African Strategies, p. 23-26 (Ohio University Press 2003)
  6. Rothmaler, Eva. Place names in Borno and Yobe States (Northern Nigeria), pp. 115, 216 (2007)
  7. Three Thousand Years in Africa, p. 200 (1981)
  8. Travels and discoveries in North and Central Africa, Vol. II, p. 585 (1857)