Abu Zamira

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Abu Zamira
Rayuwa
Sana'a
Sana'a leader (en) Fassara

Abu Zamira Mohammed shugaban ƙungiyar Boko Haram ne. Ya karɓi mulki ne bayan mutuwar Abubakar Shekau, kuma ya fara tattaunawa da gwamnatin Najeriya.[1] Ba a san matsayinsa na yanzu ba.

Mutuwar Shekau[gyara sashe | gyara masomin]

Imam Liman Ibrahim ya sanar a cikin watan Agustan shekarar 2013 cewa ƙungiyar Boko Haram ta kori Abubakar Shekau saboda munanan hanyoyinsa. Ibrahim ya kuma sanar da naɗin Abu Zamira a matsayin da Shekau ya riƙe, da kuma kawo ƙarshen dabarun tashin hankali.[2]

Tattaunawar zaman lafiya[gyara sashe | gyara masomin]

A watan Agustan 2013, Abu Zamira ya naɗa kansa da wasu mutane huɗu a matsayin wakilan Ƙungiyar Boko Haram a tattaunawar sulhu da gwamnatin Najeriya. Baya ga shi kansa tawagar ta haɗa da Abu Liman Ibrahim, Abu Adam Maisandari, Kassim Imam Biu da Malam Modu Damaturu. Waɗannan naɗe-naɗen sun kasance tare da ayyana tsagaita buɗe wuta na kwanaki 60, da kuma sanarwar cewa duk wani hari da aka kai da sunan Shekau bai inganta ba.[3]

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]