Aminu Abdullahi Shagali

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Aminu Abdullahi Shagali
Rayuwa
Haihuwa 13 ga Faburairu, 1980 (44 shekaru)
ƙasa Najeriya
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Harsuna Turanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa All Progressives Congress

Aminu Abdullahi Shagali shi ne kakakin majalisar wakilan Jihar Kaduna, Najeriya. Ya kasance shahararren dan kasuwa ne shi.

Farkon Rayuwa Da Karatu[gyara sashe | gyara masomin]

Aminu Abdullahi Shagali, an kuma haife shi ne a ranar 13 ga watan Fabrairun shekara ta alif 1980, shi ne yaro na biyar (5) a wurin mahaifinsa Alhaji Abdullahi Shagali kuma daga wurin mahaifiyarsa Hajiya Zulaihat Shagali. Ya yi karatun firamare a Bako Zuntu Nursery and Primary School, da ke Zariya a shekara ta alif (1986–1993), ya yi sakandare a Federal Government College, Daura a jihar Katsina a shekara ta alif (1993–1999), da kuma Kaduna State Polytechnic, Zariya (a yanzu ita ce Nuhu Bamalli Polytechnic) inda ya yi jarabawar Interim Joint Matriculation Board examamination a 2000. Shagali ya karanta Political Science a Jami'ar Usmanu Danfodiyo, da ke Sokoto, da yin master's degree a bangaren public administration a Jami'ar Ahmadu Bello Zaria a shekara ta 2008. Ya kuma kasance dan kasuwa ne shi gabanin tsundumarsa fagen siyasa a shekarar 2010. Bayan haka kuma ya yi karatun digiri na uku wato (PhD) a bangaren rural development a Jami'ar Bakhtalruda, da ke Sudan.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]