André Ivan Biyogo Poko (an haife shi a ranar 7 ga watan Maris a shekara ta 1993) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne na Gabon wanda kwanan nan ya taka leda a matsayin ɗan wasan tsakiya a ƙungiyar Altay ta Turkiyya da kuma ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Gabon.[1][2] Ya kasance cikin tawagar kasar Gabon a gasar AFCON ta shekarar 2021 a Kamaru.[3]
A ranar 31 ga watan Agusta shekara ta 2011, Biyogo Poko ya koma Bordeaux na Ligue 1 na Faransa kan kwantiragin shekaru uku.[4]
Ya wakilci kasarsa a gasar cin kofin kasashen Afrika a shekarar 2012, inda Gabon, a matsayin mai karbar bakuncin gasar, ta kai wasan daf da na kusa da karshe.[5][6]
↑Communiqué match No.:18 Group A matches TEAM
A: Gabon Cafonline.com
↑"Africa Cup of Nations (Sky Sports)". Sky Sports. Retrieved 9 February 2022.
↑"Transfert–André Biyogo Poko pour 3 ans".
Official site (in French). FC Girondins de Bordeaux. 31 August 2011. Archived from the original on 26
March 2012. Retrieved 10 September 2011.