Ayo Gabriel Irikefe

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Ayo Gabriel Irikefe
Chief Justice of Nigeria (en) Fassara

1985 - 1987
Rayuwa
Haihuwa Ikorodu, 3 ga Maris, 1922
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Yarbanci
Mutuwa 1 ga Augusta, 1996
Karatu
Makaranta St Gregory's College, Lagos
Harsuna Turanci
Yarbanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a mai shari'a

Chief Ayo Gabriel Irikefe, SAN OFR, CON, GCFR (Maris 3, 1922 - Agusta 1, 1996) alkalin shari'a ne dan Najeriya kuma tsohon Alkalin Alkalan Najeriya.[1]

Kuruciya[gyara sashe | gyara masomin]

An haifi Irikefe a watan Maris 1922 ga iyalin Aduwa da Theresa Irikefe. An haife shi a Ikorodu, karamar hukumar jihar Legas a kudu maso yammacin Najeriya . Ya fara karatunsa ne a makarantar CMS da ke Okitipupa, sannan ya tafi makarantar St John’s School Okitpupa, St Mathews Catholic School, Ode-Ondo da St. Gregory’s College, Obalende, Legas inda ya samu takardar shedar kammala sakandare a Yammacin Afruka.[2] Ya fara karatu a Kwalejin Marine Engineering and Communications a Manchester tsakanin 1945 zuwa 1946 kafin ya yanke shawarar yin karatun shari'a a 1949.

Aikin Shari'a[gyara sashe | gyara masomin]

An kira shi Baran Ingilishi a ranar 1 ga Yuli, 1952, a shekarar da ya kafa nasa kamfanin lauyoyi. Ya kasance yana aikin shari'a a Warri daga 1952 zuwa 1955. A shekarar 1955 ya kai matsayin mai ba da shawara a yankin yammacin Najeriya inda ya yi aiki a Ibadan sannan ya koma birnin Benin. Ya kasance babban lauya ga kwamitin da ya binciki ayyukan kungiyar asiri ta Owegbe, daga bisani kuma aka nada shi alkali a babbar kotun tsakiyar yammacin Najeriya. A shekarar 1966 ya zama Babban Lauyan Jihar Tsakiyar Yamma, mukamin da ya rike har aka nada shi kujerar Kotun Koli ta Najeriya a matsayin Mai Shari’a.[3] A shekarar 1985 ya zama memba na Nigerian Body of Benchers, a wannan shekarar ne aka nada shi a matsayin Alkalin Alkalan Najeriya inda ya gaji makamin daga hannun George Sodeinde Sowemimo.[4][5]

Irikefe ya yi ritaya a 1985 bayan ya kai shekarun yin ritaya da ka kayyaje na 65.[6]

A shekarar 1975 aka nada shi shugaban kwamitin kafa jihohi sannan kuma a shekarar 1980 aka nada Irikefe matsayin shugaban kotun sayar da danyen mai domin ya binciki zargin batan kudade a cikin kamfanin man fetur na Najeriya.[7]

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "20 reasons why Nigerians have rejected Buhari since 2003". 31 October 2014.
  2. "Federal Judicial Service Commission". fjsconline.gov.ng. Archived from the original on 2014-12-03. Retrieved 26 April 2015.
  3. Siollun, Max (2009). Oil, Politics and Violence. ISBN 9780875867106. Retrieved 26 April 2015.
  4. "Prosecutorial Powers of the Attorney-General under the Constitution: the Supreme Court erred in law and undermined the Public Interest in The State v Ilori". Sahara Reporters. 28 March 2010. Retrieved 26 April 2015.
  5. "NIGERIA'S LEADERSHIP: RATION 2:1, ANOTHER FEATHER ON JONATHAN'S CAP". TheNigerianVoice. Retrieved 26 April 2015.
  6. "NIGERIA'S LEADERSHIP: RATION 2:1, ANOTHER FEATHER ON JONATHAN'S CAP". TheNigerianVoice. Retrieved 26 April 2015.
  7. Bamgbose, Olatokunbo John (7 December 2013). Digest of Judgements of the Supreme Court of Nigeria. ISBN 9789788431404. Retrieved 26 April 2015.

Template:Chief Justices of Nigeria